< Markus 4 >

1 Ya kuma fara koyarwa a bakin teku. Akwai babban taro kewaye da shi, sai ya shiga cikin jirgin ruwa a cikin tekun, ya kuwa zauna. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun.
AND again he began to teach by the sea side: and a vast multitude was assembled about him, so that he went into a vessel to sit down on the sea, and all the multitude was on the land close by the sea.
2 Ya koya masu abubuwa da yawa da misalai, a cikin koyawarsa ya ce masu,
And he taught them in parables many things, and said unto them in the course of his teaching,
3 “ku saurara! wani mai shuka ya tafi shuka.
Hear me! Behold, a sower went out to sow;
4 Yana cikin yafa iri, sai wadansu iri suka fadi a kan hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su.
and it came to pass as he sowed, some fell by the road side, and the birds of the air came and ate it up.
5 Wadansu kuma suka fadi a kan dutse inda ba kasa dayawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin kasa.
And some fell on a rocky soil, where it had not much mold, and immediately it sprung up, because it had no depth of earth:
6 Da rana fa ta daga, sai suka yankwane da yake ba su da saiwa sosai, sai suka bushe.
and when the sun arose it was scorched up; and because it had not root, it withered away.
7 Wadansu kuma suka fadi cikin kayayuwa su ka yi girma sai kayayuwan suka shake su, ba su yi tsaba ba.
And some fell among thorns, and the thorns sprang up with it and choked it, and it produced no fruit.
8 Wadansu kuma suka fadi a kasa mai kyau, suka yi yabanya, suka yi tsaba, suka yi girma, wadansu ribi talattin wadansu sittin, wadansu kuma dari”.
And some fell on good ground, and produced fruit, growing up, and increasing, and yielded one part thirty fold, and another sixty, and another an hundred.
9 Sai ya ce, Duk mai kunnen ji, ya ji,”
And he said unto them, He that hath ears to hear, let him hear.
10 Sa'adda Yesu yake shi kadai, wadanda suke kusa dashi tare da sha biyun suka tambaye shi ma'anar misalan.
But when they were alone, those who were about him with the twelve, asked him the meaning of the parable.
11 Sai ya ce masu, “ku an yardar maku, ku san asirin mulkin Allah, amma ga wadanda ba su cikinku, komai sai a cikin Misalai,
And he said to them, To you it is given to know the mystery of the kingdom of God; but to those who are without, all things are in parables:
12 don gani da ido sun gani, amma ba su gane ba. ji kuma, sun ji, amma ba su fahimta ba, don kada su juyo a gafarta masu,”
That seeing they may see, yet not perceive; and hearing may hear, yet not understand; lest at any time they should be converted, and their sins be forgiven them.
13 Ya ce masu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misalin ba? yaushe za ku fahimci sauran?
And he saith to them, Know ye not this parable? and how will ye know all parables?
14 Mai shukan nan fa maganar Allah yake shukawa.
The sower soweth the word.
15 Wadanda suka fadi a hanyar kuwa, su ne kwatancin wadanda. a aka shuka mganar a zuciyarsu, Da suka ji, nan da nan sai shaidan ya zo ya dauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu.
Now these are they by the road side; where the word is sown; and when they have heard, immediately Satan cometh, and taketh away the word sown on their hearts:
16 Haka kuma wadanda aka shuka a wuri mai duwatsu, sune wadanda da zarar sun ji Maganar sai su karba da farin ciki.
and these in like manner are they who were sown on the rocky soil; who when they have heard the word, instantly with joy receive it;
17 Su kuwa basu da tushe, ba su da karfi, idan kunci ko tsanani ya zo saboda kalmar, nan da nan sai su yi tuntube.
and have no root in themselves, but are temporary professors: afterwards, when tribulation cometh or persecution for the word’s sake, immediately they are offended.
18 Wadansu kuma su ne kwatacin wadanda suka fadi cikin kayayuwa, sune wadanda suka ji Maganar,
And those are the sown among the thorns; such as are hearers of the word;
19 amma abubuwan duniya, da rudin dukiya da kuma kwadayin wadansu abubuwa, sukan shiga su shake Maganar, har ta zama marar amfani. (aiōn g165)
but the anxious cares of this world, and the seducing nature of wealth, and inordinate desires after other things entering in, choke the word, and it becometh unfruitful. (aiōn g165)
20 Wadanda aka shuka a kasa mai kyau kuwa, sune kwatancin wadanda suke jin Maganar, su karba, su kuma yin amfani da ita wadansu ribi talatin, wadansu sittin, wadansu dari.”
And these are they who are sown on the good ground, such as hear the word, and receive it, and bring forth fruit, some thirty fold, and some sixty, and some an hundred.
21 ya ce masu, “Shin, ana kawo fitila a cikin gida don a rufe ta da kwando ko a ajiye ta a karkashin gado? ku kan kawo ta ne don ku dora ta a kan madorinta.
And he said unto them, Is a lamp brought out to be put under a bushel, or under a bed, and not to be placed on a stand?
22 Ba abin da yake boye, da baza a sani ba ko kuma ba abinda ke asirce da bazaya bayyana a fili ba.
For there is nothing hid, but that it should be brought to light, nor is any thing concealed, but that it should come into open day.
23 Bari mai kunnen ji, ya ji!''
If any man hath ears to hear, let him hear.
24 Sai ya ce masu, ku mai da hankali a kan abin da kuka ji, Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a kara maka.
And he said unto them, Take heed what ye hear: with the measure ye mete, shall it be measured back to you; and something over shall be given to you that hear.
25 Domin mai abu akan karawa, marar abu kuma za a karba daga wurinsa a kuma karawa mai shi.”
For to him that hath, there shall more be given to him; but he that hath not, even that which he hath shall be taken away from him.
26 Sai ya ce, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a kasa.
And he said, The kingdom of heaven is of that kind, as if a man should cast seed into his field;
27 A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma bai kuwa san ta yaya aka yi ba.
and sleep and rise, night and day, and the sown corn should sprout, and grow into length, he knoweth not how:
28 Kasa da kanta, takan ba da amfani, tsiro shine ne na farko,
for the earth, naturally prolific, beareth fruit; first the blade, then the ear, then the full corn in the ear.
29 Sai kai, sa'anan sai kwaya mai kwari. Sa, adda amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi kenan.”
But when the grain is ready, immediately he putteth in the sickle, because harvest is come.
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulki Allah? ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?
And he said, To what shall I liken the kingdom of God, and under what parabolic figure shall I represent it?
31 Kamar kwayar zarra yake wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi kankanta cikin kwayoyi a duniya.
It is like a grain of mustard, which when it is sown in the earth, is among the least of all the seeds which are upon the earth:
32 Duk da haka in an shuka ta, sai ta yi girma fiye da duk sauran ita-tuwan da ke a jeji tayi manyan rassa, har tsuntsaye su iya yin sheka arassanta.”
but when it is sown, it groweth up and becomes greater than all herbaceous plants, and produceth vast branches; so that the birds of the air may roost under the shadow of it.
33 Da misalai da yawa, irin wadannan ya yi masu Magana, dadai gwargwadon ganewarsu,
And with many such like parables spake he to them the word.
34 ba ya fada masu kome sai da misali, amma a kebe, yakan bayyana wa almajiransa dukan abu.
And without a parable spake he not unto them; but in private he explained them all to his disciples.
35 A ranan nan da yama ta yi yace masu “Mu haye wancan ketaren.”
And the same day he saith unto them, as the evening shut in, Let us pass over to the other side.
36 Sai suka bar taron, suka tafi tare da shi acikin cikin jirgin. wadansu jirage kuma na tare da shi.
And sending the multitude away, they took him just as he was in the vessel; and there were also some other little vessels with him.
37 Sai babban hadari da iska mai karfi ya taso, rakuman ruwa kuma na ta girgizawa cikin jirgin, har jirgin ya cika.
And a great hurricane arose, and the waves broke into the vessel, so that it was now full of water:
38 Yesu kuwa na daga karshen bayan jirgin a kan kujera, yana barci, sai suka tashe shi, suka ce masa “Malam za mu hallaka ba ka kula ba?”
and he was in the stern, sleeping on a pillow: and they awoke him, and say unto him, Master, is it no concern to thee that we are perishing?
39 Sai ya farka, ya tsawata wa Iskar. Ya kuma ce wa ruwan tekun, “Ka natsu! ka yi shiru!” Sai Iskar ta kwanta, wurin duk ya yi shiru.
And rising, he with authority charged the wind, and said to the sea, Silence! be still! And the wind subsided, and there was a great calm.
40 Ya ce masu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu baku da bangaskiya ne?”
And he said to them, Why are ye so timorous? How is it that ye have not confidence?
41 Sai suka tsorata kwarai suka ce wa juna, “wanene wannan kuma, wanda har Iska da teku ma suke yi masa biyayya?”
And they were filled with the most reverential awe, and said one to another, What manner of man is this, that even the wind and the sea obey him?

< Markus 4 >