< Markus 16 >

1 Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana'iza.
When the Sabbath was past, Mary Magdalene, and Mary the mother of James, and Salome, bought spices, that they might come and anoint him.
2 Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.
Very early on the first day of the week, they came to the tomb when the sun had risen.
3 Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?”
They were saying among themselves, "Who will roll away the stone from the door of the tomb for us?"
4 Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.
for it was very big. Looking up, they saw that the stone was rolled back.
5 Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki.
Entering into the tomb, they saw a young man sitting on the right side, dressed in a white robe, and they were amazed.
6 Sai ya ce masu, “Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi.
He said to them, "Do not be amazed. You seek Jesus, the Nazarene, who has been crucified. He has risen. He is not here. Look, the place where they put him.
7 Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku.”
But go, tell his disciples and Peter, 'He goes before you into Galilee. There you will see him, as he said to you.'"
8 Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.
They went out, and fled from the tomb, for trembling and astonishment had come on them. They said nothing to anyone; for they were afraid.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Now when he had risen early on the first day of the week, he appeared first to Mary Magdalene, from whom he had cast out seven demons.
10 Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka.
She went and told those who had been with him, as they mourned and wept.
11 Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.
When they heard that he was alive, and had been seen by her, they disbelieved.
12 Bayan wadannan al'amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa'ilin da suke tafiya akan hanya.
And after these things he appeared in another form to two of them, as they walked on their way into the country.
13 Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.
And they went away and told it to the rest. They did not believe them, either.
14 Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu.
Afterward he was revealed to the eleven themselves as they were reclining, and he rebuked them for their unbelief and hardness of heart, because they did not believe those who had seen him after he had risen.
15 Sai ya umarcesu cewa “Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta.
And he said to them, "Go into all the world, and proclaim the Good News to the whole creation.
16 Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.
He who believes and is baptized will be saved; but he who disbelieves will be condemned.
17 Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna.
And these signs will accompany those who believe: In my name they will cast out demons; they will speak with new tongues;
18 Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa.”
they will pick up serpents; and if they drink any deadly thing, it will not harm them; they will place their hands on the sick, and they will be made well."
19 Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah.
So then the Lord Jesus, after he had spoken to them, was taken up into heaven, and sat down at the right hand of God.
20 Almajiransa kuma suka tafi ko'ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al'ajiba tare da su.
And they went out and preached everywhere, the Lord working with them and confirming the message by the signs that followed.

< Markus 16 >