< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
Muy de mañana, los principales sacerdotes consultaron con los ancianos, los escribas y el Tribunal Supremo. Ataron a Jesús, [lo] llevaron y [lo] entregaron a Pilato.
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
Pilato le preguntó: ¿Eres Tú el Rey de los judíos? Le respondió: Tú [lo ]dices.
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
Los principales sacerdotes lo acusaban mucho.
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
Pilato le preguntó otra vez: ¿Nada respondes? Mira de cuántas cosas te acusan.
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
Pero Jesús nada más respondió, de tal modo que Pilato se asombró.
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
En cada fiesta [Pilato] les soltaba un preso: el que pidieran.
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
Un hombre llamado Barrabás estaba preso con los sublevados que habían cometido un homicidio en una revuelta.
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
Cuando la multitud pidió a Pilato que hiciera lo que siempre les hacía,
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
Pilato les preguntó: ¿Quieren que les suelte al Rey de los judíos?
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
Porque entendía que los principales sacerdotes lo habían entregado por envidia.
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
Pero los principales sacerdotes incitaron a la multitud para [pedirle] que más bien les soltara a Barrabás.
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
Pilato les volvió a preguntar: ¿Qué hago al Rey de los judíos?
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
Ellos gritaron otra vez: ¡Crucifícalo!
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
Pero Pilato les preguntaba: ¿Pues qué mal hizo? Y ellos gritaron aún más: ¡Crucifícalo!
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
Pilato, entonces, quiso satisfacer a la multitud y les soltó a Barrabás. Azotó a Jesús y lo entregó para que lo crucificaran.
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
Entonces los soldados lo llevaron a la residencia oficial del gobernador y reunieron a toda la tropa.
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
Lo vistieron de púrpura, trenzaron una corona de espinas y se la pusieron [en la cabeza].
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
Lo saludaban: ¡Honores, Rey de los judíos!
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
También le golpeaban la cabeza con una caña, lo escupían y se arrodillaban para rendirle homenaje.
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
Cuando lo ridiculizaron, le quitaron la ropa de púrpura, lo vistieron con su ropa y lo sacaron para crucificarlo.
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
Obligaron a uno que pasaba, quien llegaba del campo, Simón cireneo, el padre de Alejandro y Rufo, a llevar la cruz de Jesús.
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
Lo llevaron al Gólgota, que significa: Lugar de una Calavera.
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
Le dieron vino mezclado con mirra, pero no tomó.
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
Lo crucificaron y se repartieron sus ropas para lo cual echaron suerte a fin de saber qué llevaría cada uno.
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
Eran las nueve de la mañana cuando lo crucificaron.
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
Entonces escribieron la acusación contra Él encima de la cruz: El Rey de los judíos.
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
Crucificaron con Él a dos ladrones, uno a su derecha y otro a su izquierda.
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
Los que pasaban lo ofendían, meneaban sus cabezas y decían: ¡Bah! ¡El que derriba el Santuario y [lo] reedifica en tres días,
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
baja de la cruz, sálvate a Ti mismo!
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
Del mismo modo, los principales sacerdotes y los escribas se burlaban y se decían unos a otros: Salvó a otros. Él mismo no puede salvarse.
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
¡El Cristo, el Rey de Israel! Baja ahora de la cruz para que veamos y creamos. También lo insultaban los que fueron crucificados con Él.
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
Cuando llegó el mediodía hubo oscuridad en toda la tierra hasta las tres de la tarde.
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
A esa hora Jesús exclamó a gran voz: Eloi, Eloi, ¿lema sabajtani? que significa: Dios mío, Dios mío, ¿por qué me desamparaste?
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
Al oírlo algunos de los presentes, decían: ¡Mira, llama a Elías!
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
Entonces alguien corrió y empapó una esponja con vinagre, la sujetó a una caña, le dio a beber y dijo: Dejen, veamos si Elías viene a bajarlo.
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
Pero Jesús, con una fuerte exclamación, expiró.
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
El velo del Santuario fue rasgado en dos, de arriba abajo.
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
El centurión destacado frente a Él, al ver cómo había expirado, exclamó: ¡Verdaderamente este Hombre era Hijo de Dios!
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
También estaban unas mujeres que miraban de lejos, entre quienes estaban María Magdalena, María, la madre de Jacobo el menor y de José, Salomé,
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
y muchas otras que subieron con Él a Jerusalén, las cuales lo seguían y le servían cuando estaba en Galilea.
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
Al llegar la noche, puesto que era Preparación, es decir, víspera del sábado,
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
cuando llegó José de Arimatea, miembro prominente del Tribunal Supremo, quien también esperaba el reino de Dios, con audacia entró ante Pilato y pidió el cuerpo de Jesús.
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
Pilato [se] sorprendió de que ya había muerto. Llamó al centurión para preguntar si ya había muerto.
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
Cuando el centurión le informó, [Pilato] entregó el cuerpo a José.
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
Éste compró una sábana, [lo] bajó, [lo ]envolvió en la sábana, [lo ]puso en un sepulcro excavado en una roca y rodó una piedra contra la entrada del sepulcro.
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
María Magdalena y María la [madre] de José observaban dónde era puesto.

< Markus 15 >