< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
וישכימו ראשי הכהנים עם הזקנים והסופרים וכל הסנהדרין בבקר ויתיעצו ויאסרו את ישוע ויוליכהו משם וימסרהו אל פילטוס׃
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
וישאל אותו פילטוס האתה מלך היהודים ויען ויאמר אליו אתה אמרת׃
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
וראשי הכהנים הרבו לשטנו׃
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
ויוסף פילטוס וישאלהו לאמר האינך משיב דבר ראה כמה הם מעידים בך׃
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
וישוע לא השיב עוד אף דבר אחד ויתמה פילטוס׃
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
ובכל חג היה דרכו לפטר להם אסיר אחד את אשר יבקשו׃
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
ויהי איש הנקרא בשם בר אבא אסור עם המורדים אשר רצחו רצח בעת המרד׃
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
וישא ההמון את קולו ויחלו לבקש שיעשה להם כפעם בפעם׃
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
ויען אתם פילטוס ויאמר התחפצו כי אפטר לכם את מלך היהודים׃
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
כי ידע אשר רק מקנאה מסרוהו ראשי הכהנים׃
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
וראשי הכהנים הסיתו את ההמון לבלתי פטר להם כי אם בר אבא׃
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
ויסף פילטוס ויען ויאמר להם ומה אפוא חפצתם ואעשה לאשר אתם קראים מלך היהודים׃
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
ויוסיפו לצעק הצלב אותו׃
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
ויאמר אליהם פילטוס מה אפוא עשה רעה והם הרבו עוד לצעק הצלב אותו׃
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
ויואל פילטוס לעשות כרצון העם ויפטר להם את בר אבא ואת ישוע הכה בשוטים וימסר אותו להצלב׃
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
ויוליכהו אנשי הצלב אל החצר הפנימית הוא בית המשפט ויזעיקו את כל הגדוד׃
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
וילבישהו ארגמן וישרגו עטרת קצים ויעטרהו׃
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
ויחלו לברכו לאמר שלום לך מלך היהודים׃
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
ויכו על ראשו בקנה וירקו בו ויכרעו על ברכיהם וישתחוו לו׃
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
ואחרי התלוצצם בו הפשיטו אותו את הארגמן וילבישהו את בגדיו ויוציאהו לצלב אותו׃
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
ויאנסו איש עבר אחד הבא מן השדה ושמו שמעון הקוריני אבי אלכסנדרוס ורופוס לשאת את צלבו׃
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
ויביאהו אל מקום גלגלתא הוא מקום הגלגלת׃
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
ויתנו לו יין מזוג במר והוא לא קבל׃
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
ויהי כאשר צלבו אותו ויחלקו בגדיו להם בהפילם עליהם גורל מה יקח איש איש׃
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
ותהי השעה השלישית ויצלבהו׃
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
ומכתב דבר אשמתו כתוב למעלה מלך היהודים׃
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
ויצלבו אתו שני פריצים אחד לימינו ואחד לשמאלו׃
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
וימלא הכתוב האמר ואת פשעים נמנה׃
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
והעברים גדפו אותו ויניעו ראשם לאמר האח אתה ההורס את ההיכל ובונה אותו בשלשת ימים׃
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
הושע את עצמך ורדה מן הצלב׃
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
וכן לעגו לו גם ראשי הכהנים עם הסופרים באמרם איש אל רעהו את אחרים הושיע ואת עצמו לא יוכל להושיע׃
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
המשיח מלך ישראל ירד נא מן הצלב למען נראה ונאמין וגם הנצלבים אתו חרפוהו׃
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
ובהיות השעה הששית היה חשך על כל הארץ עד השעה התשיעית׃
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
ובשעה התשיעית ויצעק ישוע בקול גדול אלהי אלהי למה שבקתני אשר פרושו אלי אלי למה עזבתני׃
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
ומקצת העמדים אצלו בשמעם את זאת אמרו הנה אל אליהו הוא קורא׃
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
וירץ אחד מהם וימלא ספוג חמץ וישם על קנה וישקהו ויאמר הניחו ונראה אם יבא אליהו להורידו׃
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
וישוע נתן קול גדול ויפח את נפשו׃
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
ופרכת ההיכל נקרעה לשנים קרעים מלמעלה למטה׃
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
וירא שר המאה העמד לנגדו כי בזעקו כן נפח את נפשו ויאמר אכן האיש הזה היה בן האלהים׃
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
וגם נשים היו שם ראות מרחוק ובתוכן גם מרים המגדלית ומרים אמו של יעקב הצעיר ושל יוסי ושלמית׃
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
אשר גם הלכו אחריו ושרתהו בהיותו בגליל ואחרות רבות אשר עלו אתו ירושלים׃
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
ועת הערב הגיע ומפני אשר ערב שבת היה הוא היום שלפני השבת׃
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
ויבא יוסף הרמתי יועץ נכבד אשר היה מחכה גם הוא למלכות האלהים ויתחזק ויבא אל פילטוס וישאל את גופת ישוע׃
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
ויתמה פילטוס על אשר הוא כבר מת ויקרא אל שר המאה וישאלהו הגוע כבר׃
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
וידע מפי שר המאה כי כן ויתן את גופתו מתנה ליוסף׃
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
והוא קנה סדין ויורד אתו ויכרכהו בסדין וישימהו בקבר חצוב בסלע ויגל אבן על פתח הקבר׃
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
ומרים המגדלית ומרים אם יוסי היו ראות את המקום אשר הושם שמה׃

< Markus 15 >