< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
Und alsbald am Morgen hielten die Hohenpriester mit den Ältesten und den Schriftgelehrten und dem ganzen Rate eine Beratung, banden Jesus, führten Ihn ab und überantworteten Ihn dem Pilatus.
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
Und Pilatus fragte Ihn: Bist Du der Juden König? Er aber antwortete und sprach zu ihm: Du sagst es.
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
Und die Hohenpriester klagten Ihn über vieles an.
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
Pilatus aber fragte Ihn wieder und sagte: Antwortest Du nicht? Siehe, wie vieler Dinge sie Dich anklagen.
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
Jesus aber antwortete nicht mehr, so daß sich Pilatus verwunderte.
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
Auf das Fest aber gab er ihnen einen Gefangenen los, um welchen sie ihn baten.
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
Es war aber einer, genannt Barabbas, mit den Aufrührern gebunden, die bei dem Aufruhr einen Mord begangen hatten.
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
Und das Volk zog hinauf und fing an ihn zu bitten, daß er ihnen täte, wie immer.
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
Pilatus aber antwortete ihnen und sprach: Wollet ihr, daß ich euch den König der Juden losgebe?
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
Denn er erkannte, daß die Hohenpriester Ihn aus Neid überantwortet hatten.
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
Aber die Hohenpriester wiegelten das Gedränge auf, daß er ihnen eher Barabbas losgäbe.
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
Pilatus aber antwortete und sprach wiederum zu ihnen: Was wollet ihr denn, daß ich mit Dem tue, Den ihr den König der Juden nennt?
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
Sie aber schrien wieder: Kreuzige Ihn!
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
Pilatus aber sprach zu ihnen: Was hat Er denn Böses getan? Sie aber schrien noch mehr: Kreuzige Ihn!
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
Pilatus aber war willens, dem Gedränge ein Genüge zu tun, und gab ihnen Barabbas los und überantwortete Jesus, nachdem er Ihn gegeißelt, daß Er gekreuzigt würde.
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
Die Kriegsknechte aber führten Ihn ab, hinein in den Hof, der das Prätorium ist, und riefen die ganze Kohorte zusammen.
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
Und sie zogen Ihm einen Purpur an, und flochten eine Dornenkrone und setzten sie Ihm auf;
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
Und fingen an, Ihn zu grüßen: Gegrüßet seist Du, König der Juden!
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
Und schlugen Ihn mit einem Rohr auf das Haupt, und spieen Ihn an, und fielen auf die Knie und beteten Ihn an.
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
Und da sie Ihn verspottet hatten, zogen sie Ihm den Purpur aus, und zogen Ihm Seine eigenen Kleider an, und führten Ihn hinaus, daß sie Ihn kreuzigten.
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
Und sie nötigten einen, Simon von Kyrene, den Vater des Alexander und Rufus, der vorüberging und vom Felde kam, daß er Ihm das Kreuz trüge.
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
Und sie führten Ihn auf die Stätte Golgatha, das ist verdolmetscht Schädelstätte.
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
Und sie gaben Ihm Myrrhenwein zu trinken, Er aber nahm ihn nicht.
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
Und da sie Ihn gekreuzigt hatten, zerteilten sie Seine Kleider, indem sie das Los über sie warfen, wer etwas nehmen solle.
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
Es war aber die dritte Stunde, und sie kreuzigten Ihn.
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
Und über Ihm war geschrieben die Überschrift von dem, wessen man Ihm Schuld gab: Der König der Juden.
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
Und mit Ihm kreuzigten sie zwei Räuber, einen zur Rechten, und einen Ihm zur Linken.
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
Und die Schrift ward erfüllt, die da sagt: Er ward unter die Missetäter gerechnet.
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
Und die da vorübergingen, lästerten Ihn, schüttelten ihre Köpfe und sagten: Ei, Du, Der Du den Tempel niedereißest und in drei Tagen bauest,
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
Rette Dich nun Selber und steige herab vom Kreuz!
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
Desgleichen spotteten auch die Hohenpriester untereinander mit den Schriftgelehrten und sagten: Er hat anderen geholfen, Sich Selber kann Er nicht helfen.
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
Der Christus, der König von Israel! Er steige jetzt herab von dem Kreuz, auf daß wir es sehen und glauben! Auch die mit Ihm Gekreuzigten schmähten Ihn.
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
Da es aber die sechste Stunde geworden, ward eine Finsternis über das ganze Land bis zur neunten Stunde.
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
Und um die neunte Stunde schrie Jesus mit großer Stimme und sprach: Elohi, Elohi, lammah sabachthani!
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
Und etliche der Dabeistehenden, die dies hörten, sprachen: Siehe, Er ruft dem Elias!
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
Einer aber lief und füllte einen Schwamm mit Essig, legte ihn um ein Rohr, tränkte Ihn, und sagte: Lasset mich, wir wollen sehen, ob Elias kommt, Ihn herbzunehmen!
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
Jesus aber schrie mit großer Stimme und hauchte aus.
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
Und der Vorhang des Tempels riß entzwei von oben bis unten.
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
Der Hauptmann aber, der dabeistand, Ihm gegenüber, sprach, als Er mit solchem Schrei verschied: Wahrhaftig, dieser Mensch war Gottes Sohn!
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
Es waren aber auch Weiber da, die von ferne zuschauten, unter denen war Maria von Magdala, und Maria, des jüngeren Jakobus und des Joses Mutter, und Salome;
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
Die Ihm auch, da Er in Galiläa war, nachfolgten und Ihm dienten, und viele andere, die mit Ihm herauf nach Jerusalem gekommen waren.
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
Und da es schon Abend ward,
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
Kam Joseph von Arimathäa, ein angesehener Ratsherr, der auch selbst auf das Reich Gottes wartete; der wagte es und ging hinein zu Pilatus und bat um den Leib Jesu.
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
Pilatus aber wunderte sich, daß Er schon gestorben wäre, und rief den Hauptmann zu sich und fragte ihn, ob Er schon eine Zeit lang gestorben wäre.
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
Und da er es vom Hauptmann erfahren, schenkte er Joseph den Leib.
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
Und er kaufte eine Leinwand, und nahm Ihn herab, wickelte Ihn in die Leinwand, und legte Ihn in eine Gruft, die aus einem Felsen gehauen war, und wälzte einen Stein auf die Tür der Gruft.
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
Aber Maria von Magdala und Maria, des Joses Mutter, schauten, wo Er hingelegt wurde.

< Markus 15 >