< Markus 15 >
1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
Dès le matin, les chefs des prêtres, auxquels s'étaient joints les Anciens et les Scribes, le Sanhédrin tout entier, qui avaient tenu conseil, chargèrent Jésus de liens, l'emmenèrent et le livrèrent à Pilate,
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
qui l'interrogea: C'est toi qui es le Roi des Juifs?» Jésus répondit ainsi: «Tu le dis.»
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
Les chefs des prêtres cependant formulaient contre lui des accusations en quantité.
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
Pilate l'interrogea une seconde fois: «Tu ne réponds rien! Vois tout ce dont on t'accuse!»
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
Mais Jésus ne répondit plus rien, ce dont Pilate, fut très surpris.
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
A chaque fête, il remettait en liberté un prisonnier, celui qu'on lui demandait.
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
Or il y en avait un nommé Bar-Abbas, emprisonné avec les séditieux qui, dans une émeute, avaient commis un meurtre.
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
La foule, étant donc montée au tribunal, se mit à demander ce qu'on lui accordait toujours.
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
Pilate alors, qui comprit que c'était par une haine jalouse que les chefs des prêtres lui avaient livré Jésus,
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
fit à la foule cette proposition: «Voulez-vous que je vous délivre «le Roi des Juifs»?
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
Mais les chefs des prêtres poussèrent la foule à demander de préférence la mise en liberté de Bar-Abbas.
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
Pilate se fit entendre de nouveau: «Que ferai-je donc de celui que vous appelez «le Roi des Juifs»?
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
Ils crièrent encore: «Crucifie-le!» —
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
«Qu'a-t-il donc fait de mal?» reprit Pilate. Mais ils n'en criaient que plus fort: «Crucifie-le!»
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
Pilate alors, voulant contenter la multitude, lui délivra Bar-Abbas, et, après avoir fait flageller Jésus, il l'abandonna au supplice de la croix.
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
Les soldats emmenèrent Jésus à l'intérieur de la cour, c'est-à-dire dans le prétoire, où ils réunirent toute la cohorte.
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
Ils l'habillèrent d'un manteau couleur de pourpre et lui mirent une couronne d'épines qu'ils avaient tressée.
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
Puis ils lui rendirent leurs hommages: «Salut! Roi des Juifs!»
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
Avec un roseau ils lui donnaient des coups sur la tète; ils crachaient sur lui, et, se mettant à genoux, ils se prosternaient devant lui.
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
Quand ils eurent fini de se moquer de lui, ils lui ôtèrent le manteau de pourpre et lui remirent ses vêtements. Ils l'emmenèrent pour le crucifier
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
et ils obligèrent un passant, un certain Simon de Cyrène, le père d'Alexandre et de Rufus, qui revenait des champs, à porter sa croix.
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
Ils le conduisirent ainsi à Golgotha, c'est un endroit dont le nom signifie: Le Crâne.
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
Là ils lui donnèrent du vin mêlé de myrrhe; mais il n'en prit pas.
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
Ils le crucifièrent, puis se partagèrent ses vêtements, en tirant au sort la part de chacun.
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
C'est à la troisième heure qu'ils le crucifièrent,
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
et l'inscription indiquant son crime était ainsi conçue: LE ROI DES JUIFS.
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
Avec lui deux brigands furent crucifiés, l'un à sa droite, l'autre à sa gauche.
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
(ainsi s'accomplit la parole de l'Ecriture: il a été compté parmi les impies.)
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
Les passants l'injuriaient; ils lui disaient, en gesticulant de la tète: «Ohé! toi qui détruis le Temple et le rebâtis en trois jours,
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
sauve-toi toi-même en descendant de la croix!»
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
Les chefs des prêtres avec les Scribes se moquaient aussi de lui et se disaient l'un à l'autre: «Il en a sauvé d'autres et il ne peut pas se sauver lui-même!» —
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
«Que «le Christ», que «le Roi d'Israël» descende maintenant de la croix, afin que nous voyions et que nous croyions!» Ceux mêmes que l'on avait crucifiés avec lui l'insultaient.
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
Quand fut venue la sixième heure, des ténèbres se firent sur tout le pays jusqu'à la neuvième heure.
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
A la neuvième heure, Jésus jeta un cri et dit d'une voix forte: «Héloï! lema sabachthanei!» ce qui signifie: «Mon Dieu! Mon Dieu! pourquoi m'as-tu abandonné?»
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
Quelques-uns des assistants l'entendant: «Le voilà qui appelle Élie», dirent-ils.
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
Il y en eut un qui courut tremper une éponge dans du vinaigre et, l'attachant à un roseau, il lui donna à boire, en disant: «Laissez et voyons si Élie va venir le descendre!»
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
Jésus cependant, ayant jeté un grand cri, expira.
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
Et le rideau du Temple se déchira en deux depuis le haut jusqu'en bas.
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
Voyant comment il avait expiré, le centurion, qui se tenait en face de lui, dit: «Cet homme-là était véritablement Fils de Dieu.»
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
Il y avait là également des femmes qui regardaient de loin. Parmi elles, Marie Magdeleine, Marie, mère de Jacques le Petit et de Josès, et Salomé,
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
qui le suivaient et le servaient lorsqu'il était en Galilée; plusieurs autres encore qui étaient montées avec lui à Jérusalem.
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
Déjà il se faisait tard, et comme c'était un jour de «Préparation», c'est-à-dire une veille de sabbat,
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
Joseph, celui qui est d'Arimathée, membre estimé du Grand-Conseil, et qui lui aussi attendait le Royaume de Dieu, alla hardiment se présenter à Pilate et lui demanda le corps de Jésus.
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
Surpris qu'il fût mort sitôt, Pilate fit appeler le centurion et lui demanda s'il était mort depuis longtemps.
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
Informé par le centurion, il donna le corps à Joseph.
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
Celui-ci, ayant acheté un linceul, descendit le corps de la croix, l'enveloppa du linceul et le déposa dans un sépulcre taillé dans le roc, puis il roula une pierre contre la porte du tombeau.
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
Or, Marie Magdeleine et Marie, mère de Josès, regardaient où on le mettait.