< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
Immediately in the morning the chief priests, with the elders and scribes, and the whole council, held a consultation, and bound Jesus, and carried him away, and delivered him to Pilate.
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
Pilate asked him, "Are you the King of the Jews?" He answered, "You say so."
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
The chief priests accused him of many things.
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
Pilate again asked him, "Have you no answer? See how many things they testify against you."
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
But Jesus made no further answer, and Pilate was amazed.
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
Now at the feast he used to release to them one prisoner, whom they requested.
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
There was one called Barabbas, bound with those who had made insurrection, who in the insurrection had committed murder.
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
And the crowd went up and began to ask him to do for them according to his custom.
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
Pilate answered them, saying, "Do you want me to release to you the King of the Jews?"
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
For he perceived that for envy the chief priests had delivered him up.
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
But the chief priests stirred up the crowd, that he should release Barabbas to them instead.
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
Pilate again asked them, "What then should I do to him whom you call the King of the Jews?"
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
They shouted again, "Crucify him."
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
Pilate said to them, "Why, what evil has he done?" But they shouted all the louder, "Crucify him."
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
Pilate, wishing to please the crowd, released Barabbas to them, and handed over Jesus, when he had flogged him, to be crucified.
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
The soldiers led him away within the court, which is the Praetorium; and they called together the whole cohort.
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
They clothed him with purple, and weaving a crown of thorns, they put it on him.
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
They began to salute him, "Greetings, King of the Jews."
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
They struck his head with a reed, and spat on him, and bowing their knees, did homage to him.
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
When they had mocked him, they took the purple off of him, and put his own garments on him. They led him out to crucify him.
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
And they forced one passing by, Simon of Cyrene, coming from the country, the father of Alexander and Rufus, to go with them, that he might carry his cross.
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
And they brought him to the place called Golgotha, which is translated, "The place of a skull."
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
They offered him wine mixed with myrrh to drink, but he did not take it.
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
Crucifying him, they parted his garments among them, casting lots on them, what each should take.
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
It was nine in the morning, and they crucified him.
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
The superscription of his accusation was written over him, "THE KING OF THE JEWS."
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
With him they crucified two robbers; one on his right hand, and one on his left.
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
And the Scripture was fulfilled which says, "And he was numbered with transgressors."
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
Those who passed by blasphemed him, wagging their heads, and saying, "Ha. You who destroy the temple, and build it in three days,
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
save yourself and come down from the cross."
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
Likewise, also the chief priests mocking among themselves with the scribes said, "He saved others. He cannot save himself.
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
Let the Messiah, the King of Israel, now come down from the cross, that we may see and believe him." Those who were crucified with him insulted him.
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
Now when it was noon, there was darkness over the whole land until three in the afternoon.
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
Then at three in the afternoon Jesus called out with a loud voice, saying, "Elohi, Elohi, lema shabachthani?" which is translated, "My God, my God, why have you forsaken me?"
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
Some of those who stood by, when they heard it, said, "Look, he is calling for Elijah."
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
One ran, and filling a sponge full of vinegar, put it on a reed, and gave it to him to drink, saying, "Let him be. Let us see whether Elijah comes to take him down."
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
Jesus gave a loud cry, and gave up the spirit.
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
The veil of the temple was torn in two from the top to the bottom.
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
And when the centurion, who stood by opposite him, saw that he cried out like this and breathed his last, he said, "Truly this man was the Son of God."
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
There were also women watching from afar, among whom were both Mary Magdalene, and Mary the mother of James the younger and of Josi, and Salome;
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
who, when he was in Galilee, followed him, and served him; and many other women who came up with him to Jerusalem.
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
When evening had now come, because it was the Preparation Day, that is, the day before the Sabbath,
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
Joseph of Arimathea, a prominent council member who also himself was looking for the Kingdom of God, came. He boldly went in to Pilate, and asked for the body of Jesus.
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
Pilate was surprised that he was already dead; and summoning the centurion, he asked him whether he had been dead long.
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
When he found out from the centurion, he granted the body to Joseph.
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
He bought a linen cloth, and taking him down, wound him in the linen cloth, and placed him in a tomb which had been cut out of a rock. He rolled a stone against the door of the tomb.
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
Mary Magdalene and Mary, the mother of Josi, saw where he was placed.

< Markus 15 >