< Markus 13 >
1 da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
AND as he went out of the temple, one of his disciples saith unto him, Master, see what manner of stones and what buildings are here!
2 Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
And Jesus answering said unto him, Seest thou these great buildings? there shall not be left one stone upon another, that shall not be thrown down.
3 Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
And as he sat upon the mount of Olives over against the temple, Peter and James and John and Andrew asked him privately,
4 Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
Tell us, when shall these things be? and what shall be the sign when all these things shall be fulfilled?
5 Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
And Jesus answering them began to say, Take heed lest any man deceive you:
6 Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
For many shall come in my name, saying, I am Christ; and shall deceive many.
7 In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
And when ye shall hear of wars and rumours of wars, be ye not troubled: for such things must needs be; but the end shall not be yet.
8 Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
For nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom: and there shall be earthquakes in divers places, and there shall be famines and troubles: these are the beginnings of sorrows.
9 Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
But take heed to yourselves: for they shall deliver you up to councils; and in the synagogues ye shall be beaten: and ye shall be brought before rulers and kings for my sake, for a testimony against them.
10 Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
And the gospel must first be published among all nations.
11 Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
But when they shall lead you, and deliver you up, take no thought beforehand what ye shall speak, neither do ye premeditate: but whatsoever shall be given you in that hour, that speak ye: for it is not ye that speak, but the Holy Ghost.
12 Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
Now the brother shall betray the brother to death, and the father the son; and children shall rise up against their parents, and shall cause them to be put to death.
13 Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
And ye shall be hated of all men for my name’s sake: but he that shall endure unto the end, the same shall be saved.
14 Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
But when ye shall see the abomination of desolation, spoken of by Daniel the prophet, standing where it ought not, (let him that readeth understand, ) then let them that be in Judæa flee to the mountains:
15 Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
And let him that is on the housetop not go down into the house, neither enter therein, to take any thing out of his house:
16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
And let him that is in the field not turn back again for to take up his garment.
17 Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
But woe to them that are with child, and to them that give suck in those days!
18 Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
And pray ye that your flight be not in the winter.
19 A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
For in those days shall be affliction, such as was not from the beginning of the creation which God created unto this time, neither shall be.
20 In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
And except that the Lord had shortened those days, no flesh should be saved: but for the elect’s sake, whom he hath chosen, he hath shortened the days.
21 To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
And then if any man shall say to you, Lo, here is Christ; or, lo, he is there; believe him not:
22 Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
For false Christs and false prophets shall rise, and shall shew signs and wonders, to seduce, if it were possible, even the elect.
23 Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
But take ye heed: behold, I have foretold you all things.
24 Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
But in those days, after that tribulation, the sun shall be darkened, and the moon shall not give her light,
25 Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
And the stars of heaven shall fall, and the powers that are in heaven shall be shaken.
26 Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
And then shall they see the Son of man coming in the clouds with great power and glory.
27 Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
And then shall he send his angels, and shall gather together his elect from the four winds, from the uttermost part of the earth to the uttermost part of heaven.
28 “Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
Now learn a parable of the fig tree; When her branch is yet tender, and putteth forth leaves, ye know that summer is near:
29 Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
So ye in like manner, when ye shall see these things come to pass, know that it is nigh, even at the doors.
30 Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Verily I say unto you, that this generation shall not pass, till all these things be done.
31 Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth shall pass away: but my words shall not pass away.
32 Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
But of that day and that hour knoweth no man, no, not the angels which are in heaven, neither the Son, but the Father.
33 Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
Take ye heed, watch and pray: for ye know not when the time is.
34 Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
For the Son of man is as a man taking a far journey, who left his house, and gave authority to his servants, and to every man his work, and commanded the porter to watch.
35 To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
Watch ye therefore: for ye know not when the master of the house cometh, at even, or at midnight, or at the cockcrowing, or in the morning:
36 Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
Lest coming suddenly he find you sleeping.
37 Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”
And what I say unto you I say unto all, Watch.