< Markus 13 >
1 da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
And as he was departing from the temple, one of his disciples said to him, “Teacher, observe these fine stones and fine structures.”
2 Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
And in response, Jesus said to him: “Do you see all these great buildings? There shall not be left stone upon stone, which is not torn down.”
3 Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
And as he sat at the Mount of Olives, opposite the temple, Peter, and James, and John, and Andrew questioned him privately.
4 Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
“Tell us, when will these things be, and what will be the sign when all these things will begin to be fulfilled?”
5 Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
And Jesus, answering, began to say to them: “See to it that no one leads you astray.
6 Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
For many will come in my name, saying, ‘For I am he,’ and they will lead many astray.
7 In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
But when you will have heard of wars and rumors of wars, you should not be afraid. For these things must be, but the end is not so soon.
8 Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
For nation will rise up against nation, and kingdom over kingdom, and there shall be earthquakes in various places, and famines. These are but the beginning of the sorrows.
9 Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
But see to yourselves. For they will hand you over to councils, and in the synagogues you will be beaten, and you shall stand before governors and kings because of me, as a testimony for them.
10 Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
And the Gospel must first be preached to all nations.
11 Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
And when they have seized you and handed you over, do not consider in advance what to say. But whatever will be given you in that hour, say that. For you will not be speaking, but the Holy Spirit.
12 Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
Then brother will betray brother to death, and the father, a son; and children will rise up against their parents and will bring about their death.
13 Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
And you will be hated by all for the sake of my name. But whoever will have persevered unto the end, the same will be saved.
14 Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
Then, when you have seen the abomination of desolation, standing where it ought not to be, let the reader understand: then let those who are in Judea flee to the mountains.
15 Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
And let whoever is on the rooftop not descend to the house, nor enter so as to take anything from the house.
16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
And let whoever may be in the field not return to take his garment.
17 Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
But woe to those who are pregnant or nursing in those days.
18 Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
Truly, pray that these things may not happen in winter.
19 A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
For those days shall have such tribulations as have not been since the beginning of the creation that God founded, even until now, and shall not be.
20 In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
And unless the Lord had shortened the days, no flesh would be saved. But, for the sake of the elect, whom he has chosen, he has shortened the days.
21 To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
And then, if anyone will have said to you: ‘Behold, here is the Christ. Behold, in that place.’ Do not believe it.
22 Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
For false Christs and false prophets will rise up, and they will present signs and wonders, so as to lead astray, if it were possible, even the elect.
23 Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
Therefore, you must take heed. Behold, I have foretold all to you.
24 Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
But in those days, after that tribulation, the sun will be darkened, and the moon will not give her splendor.
25 Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
And the stars of heaven will be falling down, and the powers that are in heaven will be moved.
26 Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
And then they shall see the Son of man arriving on the clouds, with great power and glory.
27 Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
And then he will send his Angels, and gather together his elect, from the four winds, from the limits of the earth, to the limits of heaven.
28 “Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
Now from the fig tree discern a parable. When its branch becomes tender and the foliage has been formed, you know that summer is very near.
29 Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
So also, when you will have seen these things happen, know that it is very near, even at the doors.
30 Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Amen I say to you, that this lineage shall not pass away, until all these things have happened.
31 Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth shall pass away, but my word shall not pass away.
32 Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
But concerning that day or hour, no one knows, neither the Angels in heaven, nor the Son, but only the Father.
33 Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
Take heed, be vigilant, and pray. For you do not know when the time may be.
34 Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
It is like a man who, setting out on a sojourn, left behind his house, and gave his servants authority over every work, and instructed the doorkeeper to stand watch.
35 To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
Therefore, be vigilant, for you do not know when the lord of the house may arrive: in the evening, or in the middle of the night, or at first light, or in the morning.
36 Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
Otherwise, when he will have arrived unexpectedly, he may find you sleeping.
37 Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”
But what I say to you, I say to all: Be vigilant.”