< Markus 13 >

1 da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
Og da han gik ud af Helligdommen, siger en af hans Disciple til ham: „Mester, se, hvilke Stene og hvilke Bygninger!”
2 Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
Og Jesus sagde til ham: „Ser du disse store Bygninger? der skal ikke lades Sten paa Sten, som jo skal nedbrydes.”
3 Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
Og da han sad paa Oliebjerget, lige over for Helligdommen, spurgte Peter og Jakob og Johannes og Andreas ham afsides:
4 Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
„Sig os, naar skal dette ske, og hvilket er Tegnet, naar alt dette skal til at fuldbyrdes?”
5 Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
Men Jesus begyndte at sige til dem: „Ser til, at ingen forfører eder!
6 Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
Mange skulle paa mit Navn komme og sige: Det er mig; og de skulle forføre mange.
7 In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
Men naar I høre om Krige og Krigsrygter, da lader eder ikke forskrække, thi det maa ske; men Enden er ikke endda.
8 Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
Thi Folk skal rejse sig mod Folk, og Rige mod Rige, og der skal være Jordskælv her og der, og der skal være Hungersnød og Oprør. Dette er Veernes Begyndelse.
9 Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
Men I, tager Vare paa eder selv; de skulle overgive eder til Raadsforsamlinger og til Synagoger; I skulle piskes og stilles for Landshøvdinger og Konger for min Skyld, dem til et Vidnesbyrd.
10 Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
Og Evangeliet bør først prædikes for alle Folkeslagene.
11 Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
Og naar de føre eder hen og overgive eder, da bekymrer eder ikke forud for, hvad I skulle tale; men hvad der bliver givet eder i den samme Time, det skulle I tale; thi I ere ikke de, som tale, men den Helligaand.
12 Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
Og Broder skal overgive Broder til Døden, og Fader sit Barn; og Børn skulle staa op mod Forældre og slaa dem ihjel.
13 Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
Og I skulle hades af alle for mit Navns Skyld; men den, som holder ud indtil Enden, han skal blive frelst.
14 Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
Men naar I se Ødelæggelsens Vederstyggelighed staa, hvor den ikke bør, (den, som læser det, han give Agt!) da skulle de, som ere i Judæa, fly til Bjergene;
15 Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
men den, som er paa Taget, stige ikke ned eller gaa ind for at hente noget fra sit Hus;
16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
og den, som er paa Marken, vende ikke tilbage for at hente sine Klæder!
17 Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
Men ve de frugtsommelige og dem, som give Die, i de Dage!
18 Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
Men beder om, at det ikke skal ske om Vinteren;
19 A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
thi i de Dage skal der være en saadan Trængsel, som der ikke har været fra Skabningens Begyndelse, da Gud skabte den, indtil nu, og som der heller ikke skal komme.
20 In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
Og dersom Herren ikke afkortede de Dage, da blev intet Kød frelst; men for de udvalgtes Skyld, som han har udvalgt, har han afkortet de Dage.
21 To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
Og dersom nogen da siger til eder: Se, her er Kristus, eller se der! da tror det ikke.
22 Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
Thi falske Krister og falske Profeter skulle fremstaa og gøre Tegn og Undergerninger for at forføre, om det var muligt, de udvalgte.
23 Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
Men I, vogter eder; jeg har sagt eder alt forud.”
24 Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
Men i de Dage, efter den Trængsel, skal Solen formørkes, og Maanen ikke give sit Skin,
25 Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
og Stjernerne skulle falde ned fra Himmelen, og de Kræfter, som ere i Himlene, skulle rystes.
26 Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
Og da skulle de se Menneskesønnen komme i Skyerne med megen Kraft og Herlighed.
27 Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
Og da skal han udsende sine Engle og samle sine udvalgte fra de fire Vinde, fra Jordens Ende indtil Himmelens Ende.
28 “Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
Men lærer Lignelsen af Figentræet: Naar dets Gren allerede er bleven blød, og Bladene skyde frem, da skønne I, at Sommeren er nær.
29 Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
Saaledes skulle ogsaa I, naar I se disse Ting, skønne, at han er nær for Døren.
30 Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Sandelig, siger jeg eder, denne Slægt skal ingenlunde forgaa, førend alle disse Ting ere skete.
31 Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Himmelen og Jorden skulle forgaa, men mine Ord skulle ingenlunde forgaa.
32 Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
Men om den Dag og Time ved ingen, end ikke Englene i Himmelen, heller ikke Sønnen, men alene Faderen.
33 Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
Ser til, vaager og beder; thi I vide ikke, naar Tiden er der.
34 Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
Ligesom en Mand, der drog udenlands, forlod sit Hus og gav sine Tjenere Fuldmagt, hver sin Gerning, og bød Dørvogteren, at han skulde vaage, —
35 To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
vaager derfor; thi I vide ikke, naar Husets Herre kommer, enten om Aftenen eller ved Midnat eller ved Hanegal eller om Morgenen;
36 Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
for at han ikke, naar han kommer pludseligt, skal finde eder sovende!
37 Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”
Men hvad jeg siger eder, det siger jeg alle: Vaager!”

< Markus 13 >