< Markus 12 >
1 Sai Yesu ya fara koyar da su da misalai. “Wani mutum ne ya yi gonar inabi ya shingen ta, ya haka ramin matse inabin, ya kuwa gina hasumayar tsaro. Ya ba wandansu manoma jinginar gonar, sa'an nan ya tafi wata kasa mai nisa.
Then He began to speak to them in parables: “A man planted a vineyard—put a hedge around it, dug a wine trough, built a tower—rented it to farmers and went on a journey.
2 Da lokaci ya yi, sai ya aika masu wani bawansa domin ya karbi wadansu daga cikin amfanin gonar.
At the proper time he sent a slave to the farmers, that he might receive from them some of the fruit of the vineyard.
3 Amma manoman suka kama shi, suka yin masa duka, suka kore shi hannu banza.
But they took him, beat him, and sent him away empty-handed.
4 Ya sake aikar wani bawan. Shi kuma suka raunata shi aka, suka wulakanta shi.
Again he sent another slave to them, and that one they wounded in the head by stoning, and sent him away shamefully treated.
5 Ya sake aiken wani. Shi kam, suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da wadansu da yawa, sun dodoki wadansu, suka kuma kashe wadansu.
Again he sent another, and him they killed; and many others, beating some and killing some.
6 Yanzu dai yana da sauran daya tak, shine kaunatacen dansa. Daga karshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ai za su bashi girma.
Finally, still having his one beloved son, he even sent him to them, saying, ‘They will respect my son.’
7 Amma manoman nan suka ce wa juna, “ai, wannan shine magajinsa, 'ku zo mu kashe shi, gadon ya zama namu.”
But those farmers said to one another: ‘This is the heir. Come, let's kill him and the inheritance will be ours.’
8 Sai suka kamo shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.
So they took him, killed him, and threw him out of the vineyard.
9 To, me mai gonar inabin zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba wadansu gonar.
“What therefore will the owner of the vineyard do? He will come and destroy those farmers, and give the vineyard to others.
10 Ashe, ba ku karanta wannan nassi ba? cewa, ' Dutsen da magina suka ki, shi ne ya zama mafi mahmimanci.
Have you not even read this Scripture: ‘The stone that the builders rejected, is the very one that became the cornerstone;
11 Wannan daga Ubangiji ne, kuma ya yi dai dai a idanunmu.”'
this was the Lord's doing, and it is marvelous in our eyes’?”
12 Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi masalin, amma suka ji tsoron jama'a. Don haka suka kyele shi, suka tafi.
So they started looking for a way to arrest Him, because they knew He had spoken the parable against them, but they were in fear of the crowd. Then they left Him and went away.
13 Suka aika masa da wadansu farisiyawa da Heridiyawa, don su sa masa tarko da kalamai cikin maganarsa.
Then they sent some of the Pharisees and of the Herodians to Him, in order to trap Him with a question.
14 Da suka zo, suka ce masa, “Malam, gaskiya kana koyar da maganar Allah sosai, ba ka nuna bambanci tsakani mutane, sai koyar da tafarkin Allah kake yi sosai. “Shin, mu biya haraji ga Kaisar, ko a a?”
Upon arriving they said to Him: “Teacher, we know that you are honest—you do not ‘protect’ anyone, because you do not consider the position of people, but teach the way of God in truth—is it right to pay taxes to Caesar, or not?
15 AmmaYesu ya gane munafuncinsu, ya ce masu, “Don me kuke gwada ni? ku kawo mani dinarin in gani.”
Should we pay, or should we not?” But knowing their hypocrisy, He said to them: “Why are you testing me? Bring me a denarius to look at.”
16 Suka kawowa Yesu daya. Ya ce masu, “Kamar waye da kuma rubutun wanene? suka ce masa, “Na Kaisar ne.”
So they did, and He said to them, “Whose image and inscription is this?” They said to Him, “Caesar's.”
17 Yesu ya ce, “to, ku ba Kaisar abinda yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah. Sai suka yi mamakinsa kwarai.
Then Jesus answered them by saying, “Render to Caesar the things that are Caesar's, and to God the things that are God's.” And they marveled at Him.
18 Sai Sadukiyawa suka zo wurinsa, su dake cewa babu tashin matattu. Suka tambaya shi suka ce,
Then some Sadducees came to Him—they say there is no resurrection—and asked Him, saying:
19 “Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba da, lallai ne dan'uwan mutumin ya auri matar, ya haifa wa dan'uwansa 'ya'ya.'
“Teacher, Moses wrote to us that if a man's brother dies and leaves behind a wife, but no children, then his brother should take that wife and raise up offspring for his brother.
20 To an yi wadansu 'yan'uwa maza guda bakwai, na farko ya yi aure, ya mutu bai bar 'ya'ya ba.
Well there were seven brothers. The first took a wife, and dying left no offspring.
21 Na biyu kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba 'ya'ya. Na ukun ma haka.
So the second one took her, and died; and neither did he leave any offspring. The third likewise.
22 Haka dai duk bakwai din, ba wanda ya bar 'ya'ya. A karshe kuma ita matar ta mutu.
In fact, all seven took her, and left no offspring. Last of all the woman also died.
23 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai din nan sun aure ta”.
In the resurrection, whenever they may rise, whose wife will she be?—because all seven had her as wife.”
24 Sai Yesu ya ce, “Ba saboda wannan dalili ne kuka yi kuskure ba, wato don ba ku san littafin ba, kuma ba ku san ikon Allah ba?
Then in answer Jesus said to them: “You do not know the Scriptures nor the power of God—is this not the reason that you err?
25 Domin in an tashin daga matattu, ba a aure, ba a auraswa, amma sun zama kamar malaiku a sama.
Whenever people rise from the dead, they neither marry nor are given in marriage, but are like angels in the heavens.
26 Amma game da mattattun da suka tashi, ashe, ba ku taba karantawa a littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa? “Ni ne Allah na Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu'?
But concerning the dead, that they rise, have you not read in the book of Moses, about the Bush, how God spoke to him, saying, ‘I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob’?
27 Ai, shi ba Allahn mattatu bane, amma na rayyayu ne. Hakika kun yi kuskure “.
He is not the God of dead people, but the God of living ones. You are therefore badly mistaken.”
28 Sai wani malamin attuara ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu yana ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wanne Umarni ne mafi girma dukka?”
Then one of the scribes came on the scene, heard them arguing, realized that He had answered them well, and asked Him, “Which is the first commandment of all?”
29 Yesu ya amsa yace, “mafi girma shine, 'ku saurara ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji daya ne.
Jesus answered him: “The first of all the commandments is: ‘Hear, O Israel, the Lord your (pl) God, the Lord is one;
30 Sai ka kaunaci Ubangiji Allah da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka da dukkan tunaninka, da dukkan karfinka.
and you (sg) shall love the Lord your (sg) God with all your heart and with all your soul and with all your mind and with all your strength.’ This is the first commandment.
31 ta biyu itace, 'ka kaunaci makwabcinka kamar kanka, Ba wata doka da ta fi wadannan.''
And the second, like it, is this: ‘You shall love your neighbor as yourself.’ There is no other commandment greater than these.”
32 Sai malamin attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka malam, Allah daya ne, ba kuma wani sai shi.
So the scribe said to Him: “Well said, teacher; you said truly that He is one, and there is no other except He.
33 A kaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukkan hankali, da dukkan karfi, a kuma kaunaci makwabci kamar kanka, ai ya fi dukkan hadayu na konawa.”
And to love Him with all the heart and with all the understanding and with all the soul and with all the strength, and to love the neighbor as oneself, is more than all the whole burnt offerings and sacrifices.”
34 Da Yesu ya ga ya yi masa magana da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya sake tambayarsa wani abu.
Now when Jesus saw that he answered wisely, He said to him, “You are not far from the Kingdom of God.” And after that no one dared ask Him any question.
35 Yesu ya amsa a lokacin da yake koyarwa a Haikali, ya ce “Yaya malaman attaura suke ce wa Kristi dan Dauda ne?
Then, teaching in the temple, Jesus reacted by saying: “How is it that the scribes say that the Messiah is David's son?
36 Domin Dauda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ubangiji ya ce wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na kaskantar da makiyanka'.
Because David himself said by the Holy Spirit: ‘The Lord said to my Lord, “Sit at my right hand, until I place your enemies as a stool for your feet.”’
37 Dauda da kansa ya kira shi 'Ubangiji; To, ta yaya ya Almasihu zai zama Dan Dauda?” Babban taron jama'ar suka saurare shi da murna.
Therefore David himself calls Him ‘Lord’; so how can He be his son?” The large crowd listened to Him with pleasure.
38 A koyarwa sa Yasu ya ce, “ku yi hankali da malaman attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishesu a kasuwa,
Then He said to them in His teaching: “Beware of the scribes, who like to walk about in long robes and to get greetings in the market places,
39 da kuma son wuraren zama masu daraja a haikali, da wurin bukukuwa.
and the best seats in the synagogues, and the best places at feasts;
40 Sun kuma kwace gidajen gwauraye, da yin doguwar addu'a, don mutane su gani. Wadanan mutanen zasu sami hukunci mai tsanani.”
who devour the houses of widows, while praying long and loud for a show. These will receive a more severe judgment.”
41 Sai ya zauna a gaban akwatin baiko a Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kudi a ciki.
Then Jesus sat down opposite the offering chest and started watching how the people were depositing money into the chest. Many rich people put in large amounts.
42 Wadansu masu arziki da yawa suna zuba kudi masu tsoka. Sai gwauruwa mara abin hanu ta saka anini biyu a ciki akwatin baikon.
A certain poor widow also came and put in two ‘lepta’, which equal a ‘quadrans’.
43 Ya kira almajiransa, ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, abinda gwauruwa nan ta saka a akwatin baikon nan ya fi na sauran dukka.
So summoning His disciples He said to them: “I tell you assuredly that this poor widow has put more in the chest than all these contributors;
44 Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta bada duk abinda take da shi.”
because they all gave out of their excess, but she, out of her lack, put in all that she had, her whole livelihood.”