< Markus 11 >

1 Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu
And when they came nye to Hierusalem vnto Bethphage and Bethanie besydes mout olivete he sent forth two of his hisciples
2 ya ce masu, “ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani.
and sayde vnto the: Goo youre wayes into the toune that is over agaynst you. And assone as ye be entred into it ye shall fynde a coolte bounde wheron never man sate: loose him and bringe him.
3 In wani ya ce maku, “Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan.”'
And if eny man saye vnto you: why do ye soo? Saye that the Lorde hath neade of him: and streight waye he will sende him hidder.
4 Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.
And they wet their waye and foud a coolte tyed by the dore with out in a place where two wayes met and they losed him.
5 sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, “Don me kuke kwance aholakin nan?
And divers of the that stode there sayde vnto the: what do ye loosinge ye coolte?
6 Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.
And they sayd vnto them eve as Iesus had comaunded the. And they let them goo.
7 Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau.
And they brought ye coolte to Iesus and caste their garmetes on him: and he sate vpo him.
8 Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen.
And many sprede there garmetes in the waye. Other cut doune brauches of the trees and strawed them in ye waye.
9 Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.
And they yt went before and they that folowed cryed sayinge: Hos anna: blessed be he that cometh in ye name of ye Lorde.
10 Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!”
Blessed be ye kingdome that cometh in ye name of him yt is Lorde of oure father David. Hos anna in ye hyest.
11 San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan.
And ye Lorde entred in to Ierusalem and into the teple. And when he had loked roudabout vpon all thinges and now ye eve tyde was come he went out vnto Bethany with ye twelve.
12 Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.
And on the morowe when they were come out fro Bethany he hungred
13 Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.
and spyed a fygge tree a farre of havinge leves and wet to se whether he myght finde eny thinge ther on. But when he came therto he foude no thinge but leves: for the tyme of fygges was not yet.
14 Sai ya ce wa bauren, “Kada kowa ya kara cin ''ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa sun ji maganar. (aiōn g165)
And Iesus answered and sayde to it: never man eate frute of the here after whill ye worlde stondith. And his disciples hearde it. (aiōn g165)
15 Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru.
And they came to Ierusalem. And Iesus wet into the teple and begane to cast out ye sellers and byers in the teple and overthrewe the tables of the money chaungers and the stoles of them that solde doves:
16 Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.
and wolde not suffre that eny man caried a vessell thorow the temple.
17 Sai ya koyar da su cewa, “Ashe ba rubuce yake ba, “Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi”.
And he taught sayinge vnto them is it not written: my housse shalbe called the housse of prayer vnto all nacions? But ye have made it a deen of theves.
18 Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa.
And the Scribes and hye prestes hearde yt and sought howe to distroye him. For they feared him because all the people marveled at his doctrine.
19 Kowace yamma kuma, sukan fita gari.
And when eve was come he went out of the cite.
20 Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe.
And in the mornynge as they passed by they sawe the fygge tree dryed vp by ye rotes.
21 Bitrus kuwa ya tuna ya ce “Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe.”
And Peter remembred and sayde vnto him: master beholde the fygge tree which thou cursedest is widdred awaye.
22 Yesu ya amsa masu ya ce, “ku gaskata da Allah.”
And Iesus answered and sayde vnto them: Have confides in God.
23 Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.
Verely I saye vnto you that whosoever shall saye vnto this mountayne: take awaye thy silfe and cast thy silfe in to the see and shall not waver in his herte but shall beleve yt those thinges which he sayeth shall come to passe what soever he sayeth shalbe done to him.
24 Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku.
Therfore I saye vnto you what soever ye desyre when ye praye beleve yt ye shall have it and it shalbe done vnto you.
25 Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi.”
And when ye stod and praye forgeve yf ye have eny thinge agaynste eny man yt youre father also which is in heve maye forgeve you youre trespases.
26 (Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)
27 Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa,
And they came agayne to Hierusalem. And as he walked in the teple ther came to him ye hye prestes and the Scribes and the elders
28 suka ce masa, “Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu? “
and sayd vnto him: by what auctorite doest thou these thinges? and who gave the this auctorite to do these thinges?
29 Sai Yesu ya ce masu, “Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan.
Iesus answered and sayde vnto them: I will also axe of you a certayne thinge: and answere ye me and I wyll tell you by what auctorite I do these thinges.
30 Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa”.
The baptyme of Iohn was it from heven or of men? Answer me.
31 Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, “in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, “To, don me ba ku gaskata shi ba?
And they thought in them selves sayinge: yf we shall saye from heven: he will saye why then dyd ye not beleve him?
32 In kuwa muka ce, “amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.
but if we shall saye of me: then feare we ye people. For all men counted Iohn that he was a verie Prophete.
33 Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba” Yesu ya ce masu, “Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba.”
And they answered and sayd vnto Iesu: we cannot tell. And Iesus answered and sayd vnto them: nether wyll I tell you by what auctorite I do these thynges.

< Markus 11 >