< Markus 10 >
1 Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa.
And he arose and went thence into the borders of Judea, by the other side of the Jordan. And the multitudes again came together to him; and, as his custom was, he taught them again.
2 Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, '' dai dai ne mutum ya saki matarsa?'' Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi.
And the Pharisees came to him, and that they might tempt him, asked him the question: Is it lawful for a man to put away his wife?
3 Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku?
He answered and said to them: What commandment did Moses give you?
4 Suka ce, ''Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita.''
They replied: Moses permitted us to write a bill of divorce, and put her away.
5 “Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar,” Yesu ya ce masu.
And Jesus answered and said to them: On account of the hardness of your hearts, he wrote this commandment for you.
6 Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'
But from the beginning of the creation, God made them male and female.
7 Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa.
For this cause shall a man leave his father and mother, and shall be joined to his wife;
8 Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba,
and the two shall be one flesh. So, then, they are no longer two, but one flesh.
9 Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba.”
Therefore, what God has joined together, let not man put asunder.
10 Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana.
And in the house, his disciples again asked him about the same matter.
11 Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan.
And he said to them: Whoever puts away his wife, and marries another, commits adultery against her;
12 Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan.”
and if a woman puts away her husband, and is married to another, she commits adultery.
13 Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su.
And they brought little children to him, that he might touch them: but his disciples rebuked those who brought them.
14 Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.
And when Jesus saw it, he was displeased, and said to them: Let the little children come to me, and forbid them not; for of such is the kingdom of God.
15 Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba.
Verily I say to you, Whoever will not receive the kingdom of God as a little child, shall not enter into it.
16 Sai ya rungume su ya sa masu albarka.
And he took them in his arms, laid his hands on them, and blessed them.
17 Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya ''Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?'' (aiōnios )
And as he was going forth into the road, one ran and bowed the knee to him, and asked him: Good Teacher, what shall I do that I may inherit eternal life? (aiōnios )
18 Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai.
Jesus said to him: Why do you call me good? None is good but one, that is God.
19 Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
You know the commandments, You shall not commit adultery; You shall not kill; You shall not steal; You shall not give false testimony; You shall not defraud; Honor your father and mother.
20 Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro.
He answered and said to him: Teacher, all these I have kept from my youth.
21 Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.
And Jesus, looking on him, loved him, and said to him: One thing you lack; go, sell whatever you have, and give to the poor, and you shall have treasure in heaven: and come, take up the cross, and follow me.
22 Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.
But becoming sad at that saying, he went away sorrowful: for he had great possessions.
23 Yesu ya dubi almajiransa ya ce. ''Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!''
And Jesus looked around, and said to his disciples: With what difficulty will those who have riches enter into the kingdom of God!
24 Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah.
And his disciples were amazed at his words. But Jesus, answering again, said to them: Children, how hard it is for those who trust in riches to enter the kingdom of God!
25 Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.
It is easier for a camel to go through the eye of a needle, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
26 Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, ''to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?''
And they were astonished beyond measure, and said among themselves: Who, then, can be saved?
27 Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne.
Jesus looked on them and said: With men this is impossible, but not with God; for with God all things are possible.
28 Bitrus ya ce masa, ''to gashi mu mun bar kome, mun bika''.
And Peter began to say to him: Behold, we have left all and followed thee.
29 Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara,
And Jesus answering, said: Verily I say to you, There is no one that has left house, or brothers, or sisters, or father, or mother, or wife, or children, or lands, for my sake, and for the sake of the gospel,
30 sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
who shall not receive a hundred-fold, now in this time, houses and brothers and sisters and mothers and children and lands, with persecutions; and in the age to come, eternal life. (aiōn , aiōnios )
31 Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.
But many that are first shall be last; and the last first.
32 Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi.
And they were in the road going up to Jerusalem; and Jesus went before them; and they were amazed, and as they followed, they were afraid. And again taking the twelve aside, he began to tell them what was about to befall him.
33 “Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai.
Behold, we are going up to Jerusalem, and the Son of man will be delivered to the chief priests and the scribes, and they will condemn him to death, and deliver him to the Gentiles;
34 Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi.”
and they will deride him, and scourge him, and spit upon him, and kill him, and on the third day he will rise again.
35 Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, ''Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka''
And James and John the sons of Zebedee came to him, and said: Teacher, we desire you to do for us whatever we shall ask.
36 Ya ce masu. ''Me ku ke so in yi maku?''
He said to them: What do you wish me to do for you?
37 Suka ce, ''ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka.''
They said to him: Grant to us that we may sit, one on thy right hand, and one on thy left, in thy glory.
38 Yesu ya ce masu. ''Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?''
Jesus said to them: You know not what you ask. Are you able to drink the cup that I drink, and to be immersed with the immersion with which I am immersed?
39 Suka fada masa, ''Zamu iya.'' Yesu ya ce masu, '' kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku.''
They said to him: We are able. Jesus said to them: You shall drink the cup that I drink, and you shall be immersed with the immersion with which I am immersed.
40 Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne.”
But to sit on my right hand and on my left, is not mine to give; but it shall be given to those for whom it is prepared.
41 Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.
And when the ten heard it, they began to be displeased with James and John.
42 Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, '' kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.
But Jesus called them to him, and said to them: You know that those who think they rule the Gentiles, act as lords over them; and their great men exercise authority over them.
43 Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.
But it shall not be so among you. But whoever desires to be great among you, shall be your minister;
44 Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa.
and whoever among you desires to be first, shall be servant of all.
45 Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa.”
For the Son of man came not to be ministered to, but to minister, and to give his life a ransom for many.
46 Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya.
And they came to Jericho: and as he was going out of Jericho, with his disciples and a great multitude, blind Bartimæus, the son of Timæus, was sitting on the roadside, begging.
47 Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, ''Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina''
And when he heard that it was Jesus the Nazarene, he began to cry out and say: Jesus, son of David, have mercy on me!
48 Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!”
And many rebuked him, that he should be silent. But he cried out yet the more: Son of David, have mercy on me!
49 Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. ''Albishrinka, ta so! Yana kiranka.''
And Jesus stood still, and commanded him to be called. And they called the blind man, and said to him: Take courage; arise, he calls you.
50 Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.
And throwing away his mantle, he arose, and came to Jesus.
51 Yesu ya tambaye shi, ya ce, '' me ka ke so in yi maka?'' Makahon ya ce, ''Malam in sami gani.''
And Jesus answered and said to him: What do you wish me to do for you? The blind man said to him: Rabboni, that I may receive my sight.
52 Yesu ya ce masa. ''Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.'' Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.
And Jesus said to him: Go, your faith has saved you. And he immediately received his sight, and followed Jesus on the road.