< Luka 1 >
1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Juba mitmed on võtnud ette koostada ülevaadet neist asjust, mis meie seas on täide viidud,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
kooskõlas sellega, kuidas pealtnägijad ja sulased need on meile edasi andnud.
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
Nõnda olen minagi otsustanud, kuna ma olen algusest peale kõik täpselt järele uurinud, kirjutada korralik ülevaade sulle, kõrgesti austatud Teofilos,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
et sa teaksid, kui usaldusväärne on sulle antud õpetus.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
Juuda kuninga Heroodese ajal elas Sakariase nimeline preester, Abija teenistuskorrast. Tema naine oli Aaroni järeltulija ja naise nimi oli Eliisabet.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Nad mõlemad olid õiged Jumala silmis, elades laitmatult kõigis Issanda käskudes ja korraldustes.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Aga neil ei olnud last, sest Eliisabet oli viljatu, ja nad mõlemad olid eakad.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Kord aga, kui Sakarias oli oma teenistuskorra ajal preestritalituses Jumala ees,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
langes talle liisk minna preestrite kombe kohaselt Issanda templisse viirukit suitsutama.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Ja kui viiruki suitsutamise aeg saabus, palvetas kokku tulnud rahvahulk väljas.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Siis ilmus talle Issanda ingel, seistes suitsutusaltari paremal pool.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Teda nähes Sakarias ehmus ja teda valdas hirm.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Kuid ingel ütles talle: „Ära karda, Sakarias, sest su palvet on kuuldud. Su naine Eliisabet sünnitab sulle poja, ja sa paned talle nimeks Johannes.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Sul on temast rõõmu ja hõiskamist ning paljud rõõmustavad tema sündimisest,
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
sest ta saab suureks Issanda silmis. Ta ei tohi juua veini ega teisi kääritatud jooke, ja ta täidetakse Püha Vaimuga juba enne sündimist emaihus.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Ta pöörab palju Iisraeli rahvast tagasi Issanda, nende Jumala poole.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Ta kõnnib Issanda ees Eelija vaimus ja väes, et pöörata vanemate südamed nende laste poole ja sõnakuulmatud õigete tarkusse, et valmistada rahvas ette Issanda jaoks.“
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Sakarias küsis inglilt: „Kuidas ma saan selles kindel olla? Ma olen juba vana mees ja mu nainegi on eakas.“
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Ingel vastas talle: „Mina olen Gaabriel, kes seisab Jumala ees, ja mind on läkitatud sinuga rääkima ja kuulutama sulle seda rõõmusõnumit.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Nüüdsest jääd sa tummaks ega saa rääkida päevani, mil need asjad sünnivad, sest sa ei uskunud mu sõnu, mis lähevad täide määratud ajal.“
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Samal ajal ootas rahvas Sakariast ja pani imeks, et ta nii kaua templis viibib.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Kui ta lõpuks välja tuli, siis ei saanud ta nendega rääkida. Nad mõistsid, et ta oli templis näinud nägemust, sest ta viipas neile käega, kuid ei suutnud rääkida.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Kui Sakariase teenistuskord läbi sai, läks ta koju.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Mõne aja pärast jäi ta naine Eliisabet lapseootele ja tõmbus viieks kuuks üksindusse. Ta ütles:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
„Nõnda on Issand mulle neil päevil teinud, et ta näitas mulle oma soosingut ning võttis ära mu häbi inimeste ees.“
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Kuue kuu pärast läkitas Jumal ingel Gaabrieli Naatsareti linna Galileas,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
neitsi juurde, kelle nimi oli Maarja. Maarja oli kihlatud Joosepiga, kes põlvnes Taaveti soost.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Gaabriel läks tema juurde ja ütles: „Ole tervitatud, sa armuleidnu! Issand on sinuga!“
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Maarja kohkus väga neist sõnadest ja mõtles, mida see tervitus võiks tähendada.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Aga ingel ütles talle: „Ära karda, Maarja, sest sa oled leidnud armu Jumala silmis!
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Sa jääd lapseootele ja sünnitad poja ja paned talle nimeks Jeesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Tema saab suureks ja teda kutsutakse Kõigekõrgema Pojaks ning Issand Jumal annab talle tema esiisa Taaveti trooni.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
Ta valitseb kuningana Jaakobi soo üle igavesti ning tema valitsus ei lõpe iialgi.“ (aiōn )
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Maarja küsis inglilt: „Kuidas see võimalik on, kui ma olen neitsi?“
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Ingel vastas talle: „Püha Vaim tuleb sinu peale ja Kõigekõrgema vägi katab sind. Seepärast on laps, kes sinust sünnib, Püha, ja teda kutsutakse Jumala Pojaks.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Isegi su sugulane Eliisabet on pojaootel oma vanas eas ja see on kuues kuu temal, keda öeldi olevat viljatu.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Sest Jumala käes ei ole ükski asi võimatu.“
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Maarja ütles: „Mina olen Issanda teenija, sündigu mulle nii, nagu sa ütlesid!“Ja ingel läks tema juurest ära.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Neil päevil asus Maarja teele ja ruttas mäestikku Juuda linna.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Ta läks Sakariase majja ja tervitas Eliisabetti.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Kui Eliisabet kuulis Maarja tervitust, hüppas laps tema üsas ja Eliisabet sai täis Püha Vaimu.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Ta hüüdis valju häälega: „Õnnistatud oled sina naiste seas ja õnnistatud on laps, keda sa kannad!
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Aga miks saab mulle osaks selline arm, et mu Issanda ema tuleb minu juurde?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Niipea kui su tervituse hääl mu kõrvu kostis, hüppas laps mu ihus rõõmu pärast.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Õnnistatud on see, kes on uskunud, et Issand täidab oma tõotused, mis ta on lubanud!“
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Maarja ütles: „Mu hing ülistab Issandat
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
ja mu vaim hõiskab Jumalas, minu Päästjas,
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
sest ta on pannud tähele oma sulase alandlikku olekut. Siitpeale hüüavad mind õnnistatuks kõik sugupõlved,
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
sest mulle on suuri asju teinud Vägev. Tema nimi on püha,
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
tema halastus ulatub nendeni, kes teda kardavad, sugupõlvest sugupõlveni.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Ta on teinud vägevaid tegusid oma käega, ta on pillutanud laiali need, kes on uhked oma mõtetes.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Ta on tõuganud maha valitsejad aujärgedelt ja ülendanud alandlikke.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Näljased on ta täitnud heade andidega, ent rikkad saatnud tühjalt minema.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Ta on kandnud hoolt oma sulase Iisraeli eest, ja osutanud halastust,
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
nõnda nagu ta on lubanud meie esivanematele, Aabrahamile ja tema järeltulijatele igavesti.“ (aiōn )
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Maarja jäi Eliisabeti juurde umbes kolmeks kuuks ja pöördus siis tagasi koju.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Kui Eliisabetil tuli aeg sünnitada, tõi ta ilmale poja.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Tema naabrid ja sugulased kuulsid, et Issand oli osutanud talle suurt halastust, ja nad rõõmustasid koos temaga.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Nad tulid kaheksandal päeval lapse ümberlõikamisele ja tahtsid panna talle tema isa nime Sakarias.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Kuid lapse ema ütles: „Ei, tema nimi peab olema Johannes!“
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Nad ütlesid talle: „Su suguvõsas pole kedagi sellenimelist!“
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Ja nad viipasid lapse isale, küsides, mis nime tema tahab lapsele panna.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Sakarias küsis tahvlit ning kirjutas kõigi imestuseks: „Tema nimi on Johannes!“
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Samal hetkel pääsesid ta keelepaelad valla ja ta hakkas rääkima, kiites Jumalat.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Aukartus valdas kõiki naabreid ja neist asjust räägiti kogu Juuda mägismaal.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Kõik, kes sellest kuulsid, imestasid ja küsisid: „Mis küll saab sellest lapsest?“Sest Issanda käsi oli temaga.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Lapse isa Sakarias sai täis Püha Vaimu ja prohveteeris:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
„Kiidetud olgu Issand, Iisraeli Jumal, et ta on tulnud oma rahva hulka ja nad lunastanud.
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
Ta on meile üles tõstnud päästesarve oma sulase Taaveti soost,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
nagu ta on rääkinud ajastute algusest oma pühade prohvetite suu kaudu, (aiōn )
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
pääste meie vaenlaste käest ja kõigi vihameeste käest,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
et armu anda meie vanematele ja pidada meeles oma püha lepingut,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
vannet, mille ta on vandunud meie esiisale Aabrahamile:
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
päästa meid meie vaenlaste käest ja lubada meil teda kartmatult teenida
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
pühaduses ja õigluses tema ees kõik meie elupäevad.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Ja sind, minu laps, hüütakse Kõigekõrgema prohvetiks, sest sa lähed Issanda ees temale teed valmistama,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
et anda tema rahvale teada päästest nende pattude andeksandmises,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
meie Jumala südamliku halastuse läbi, millega meile tuleb päikesetõus taevast,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
et paista nende peale, kes elavad pimeduses ja surma varjus ja juhtida meie jalgu rahuteele.“
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Aga laps kasvas ja sai tugevaks vaimus. Ta elas kõrbes selle päevani, mil ta astus avalikult Iisraeli ette.