< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Since many have undertaken to compile an account of the events that have been fulfilled among us,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
just as those who from the beginning were eyewitnesses and ministers of the word have delivered them to us,
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
it seemed good to me also, having carefully investigated all things from the beginning, to write an orderly account for yoʋ, most excellent Theophilus,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
so that yoʋ may know the certainty of the things about which yoʋ have been instructed.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
In the days of Herod, the king of Judea, there was a priest named Zechariah who belonged to the division of Abijah. His wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
They were both righteous before God, walking blamelessly in all the commandments and regulations of the Lord.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
But they had no children because Elizabeth was barren, and they were both advanced in their days.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
While Zechariah was serving as a priest before God when his division was on duty,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
he was chosen by lot, according to the custom of the priesthood, to enter the temple of the Lord and burn incense.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
At the hour of incense a great crowd was assembled outside, praying.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Then an angel of the Lord appeared to Zechariah, standing at the right side of the altar of incense.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
When Zechariah saw him, he was startled, and fear fell upon him.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah, for yoʋr prayer has been heard. Yoʋr wife Elizabeth will bear yoʋ a son, and yoʋ shall name him John.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Yoʋ will have joy and gladness, and many will rejoice at his birth,
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
for he will be great in the sight of the Lord. He must never drink any wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
He will turn many of the sons of Israel to the Lord their God.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
And he will go before the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of fathers back to their children, and the disobedient to the wisdom of the righteous, to make ready a people prepared for the Lord.”
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Zechariah said to the angel, “How can I know this for certain? For I am an old man, and my wife is advanced in her days.”
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
The angel answered him, “I am Gabriel. I stand in the presence of God and was sent to speak to yoʋ and bring yoʋ this good news.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
But behold, yoʋ will be silent and unable to speak until the day these things take place, because yoʋ did not believe my words, which will be fulfilled at their appointed time.”
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Meanwhile, the people were waiting for Zechariah and wondering about his delay in the temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
When he came out, he was unable to speak to them, and they perceived that he had seen a vision in the temple, because he kept making signs to them and remained unable to speak.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
And when the days of his service had come to an end, he returned to his home.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
After those days his wife Elizabeth conceived and kept herself in seclusion for five months, saying,
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“The Lord has done this for me. In these days he has looked upon me with favor and taken away my reproach among the people.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
In the sixth month the angel Gabriel was sent by God to a town of Galilee called Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
to a virgin betrothed to a man named Joseph, of the house of David. The virgin's name was Mary.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
The angel came to her and said, “Greetings, O favored one, the Lord is with yoʋ! Blessed are yoʋ among women!”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
But when Mary saw him, she was greatly perplexed by his statement and began wondering what sort of greeting this could be.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Then the angel said to her, “Do not be afraid, Mary, for yoʋ have found favor with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
And behold, yoʋ will conceive in yoʋr womb and give birth to a son, and yoʋ shall name him Jesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
He will be great and will be called the Son of the Most High, and the Lord God will give him the throne of his father David.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
He will reign over the house of Jacob forever, and of his kingdom there will be no end.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Mary said to the angel, “How will this be, since I am a virgin?”
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
The angel answered her, “The Holy Spirit will come upon yoʋ, and the power of the Most High will overshadow yoʋ; therefore the holy child that is to be born will be called the Son of God.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
And behold, yoʋr relative Elizabeth has also conceived a son in her old age, and this is the sixth month for her who was called barren.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
For nothing is impossible with God.”
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Then Mary said, “Behold, I am the servant of the Lord; may it happen to me according to yoʋr word.” And the angel left her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
In those days Mary arose and went with haste to the hill country, to a town of Judah,
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
where she entered the house of Zechariah and greeted Elizabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
When Elizabeth heard Mary's greeting, the baby leaped in her womb, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Then she exclaimed with a loud voice, “Blessed are yoʋ among women, and blessed is the fruit of yoʋr womb!
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
How has this happened to me that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For behold, when the sound of yoʋr greeting came into my ears, the baby in my womb leaped for joy.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Blessed is she who has believed, for what the Lord has spoken to her will be fulfilled.”
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Then Mary said, “My soul magnifies the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
and my spirit rejoices in God my Savior,
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
because he has looked favorably on the humble state of his servant. For behold, from now on all generations will call me blessed,
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
because the Mighty One has done great things for me; holy is his name.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
From generation to generation his mercy is upon those who fear him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
He has done a mighty deed with his arm; he has scattered the proud in the thoughts of their hearts.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
He has brought down rulers from their thrones and exalted the lowly.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent away empty.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
He has helped his servant Israel, remembering his mercy,
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
just as he spoke to our fathers, to Abraham and to his offspring forever.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
And Mary remained with Elizabeth for about three months and then returned to her house.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Now the time was fulfilled for Elizabeth to give birth, and she bore a son.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Then her neighbors and her relatives heard that the Lord had magnified his mercy with her, and they rejoiced with her.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
On the eighth day they came to circumcise the child, and they were going to name him Zechariah, after his father.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
But the child's mother responded, “No! He is to be called John.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
But they said to her, “There is no one among yoʋr relatives who has that name.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Then they began making signs to the child's father to find out what he wanted to name him.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
So he asked for a tablet and wrote, “His name is John.” And they were all amazed.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
At once Zechariah's mouth was opened and his tongue was released, and he began to speak, blessing God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Then fear came upon all who dwelt around them, and in the entire hill country of Judea all these things were being discussed.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
All who heard about this laid it up in their hearts, saying, “What then will this child become?” And the hand of the Lord was with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Then Zechariah, the child's father, was filled with the Holy Spirit and prophesied:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Blessed be the Lord, the God of Israel, for he has visited his people and brought them redemption.
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
He has raised up for us a horn of salvation in the house of his servant David
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
(just as he spoke through the mouth of his holy prophets long ago), (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
salvation from our enemies and from the hand of all who hate us—
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
to deal mercifully with our fathers and to remember his holy covenant,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
the oath he swore to Abraham our father, to grant us
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
that we, having been rescued from the hands of our enemies, might serve him without fear,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
in holiness and righteousness before him all the days of our lives.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
And yoʋ, child, will be called a prophet of the Most High, for yoʋ will go before the presence of the Lord to prepare his ways,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
to give his people knowledge of salvation through the remission of their sins,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
through the tender mercy of our God, by which the sunrise has visited us from on high,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
to give light to those who sit in darkness and in the shadow of death, to guide our feet into the way of peace.”
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
And the child grew and became strong in spirit, and he was in the wilderness until the day of his public appearance to Israel.

< Luka 1 >