< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Since many have undertaken to compose a history of the things that are fully believed among us,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
even as they were delivered to us by those who were, from the beginning, eye-witnesses and ministers of the word;
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
it seemed good to me also, having obtained exact information of all things from the very first, to write them in order for you, most excellent Theophilus,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
that you might know the certainty of the things in which you have been instructed.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
There was, in the days of Herod the king of Judea, a certain priest, named Zachariah, of the class of Abijah; and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
They were both righteous before God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord, blameless.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both advanced in years.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
It came to pass, while he was officiating as priest before God, in the order of his class, that,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
according to the custom of the priest’s office, his lot was to burn incense, when he went into the temple of the Lord.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
And all the multitude of the people were praying without, at the time of incense.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
And there appeared to him an angel of the Lord, standing at the right side of the altar of incense.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
And Zachariah was troubled at the sight, and fear fell upon him.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the angel said to him: Fear not, Zachariah; for your prayer is heard, and your wife Elizabeth shall bear you a son, and you shall call his name John.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
And you shall have joy and gladness, and many shall rejoice at his birth.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
For he shall be great before the Lord; and he shall drink neither wine nor strong drink; and he shall be filled with the Holy Spirit even from his mother’s womb.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
And many of the sons of Israel shall he turn to the Lord their God.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
And he shall go before him in the spirit and power of Elijah to turn the hearts of the fathers to the children, and the disobedient, by the wisdom of the just, in order to make ready for the Lord a prepared people.
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
And Zachariah said to the angel: By what sign shall I know this? for I am old, and my wife is advanced in years.
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
And the angel answered and said to him: I am Gabriel, who stands in the presence of God; and I am sent to speak to you, and to announce to you this good news.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
And behold, you shall be dumb and not able to speak, till the day in which these things shall take place, because you did not believe my words, which shall be fulfilled in their proper time.
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
And the people were waiting for Zachariah, and they wondered that he stayed so long in the temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
But when he came out, he was not able to speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the temple; and he made signs to them, and remained speechless.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
And it came to pass, when the days of his service were completed, that he departed to his own house.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
And after those days, his wife Elizabeth conceived, and kept herself retired for five months, saying:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
Thus has the Lord dealt with me in the days in which he has looked with regard upon me, to take away my reproach among men.
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
And in the sixth month, the angel Gabriel was sent from God into a city of Galilee, named Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the name of the virgin was Mary.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
And the angel came into her presence, and said: Hail, graciously accepted: the Lord is with you; blessed are you among women.
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
And she was perplexed at his words, and reasoned, what this salutation could mean.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
And the angel said to her: Fear not, Mary; for you have found favor with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
And behold, you shall conceive and bear a son, and you shall call his name Jesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
He shall be great, and shall be called the Son of the Most High; and the Lord God will give to him the throne of David his father;
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
and he shall reign over the house of Jacob forever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
But Mary said to the angel: How shall this be, since I know not a man?
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
And the angel answered and said to her: The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you; for which reason, also, that which is begotten, being holy, shall be called the Son of God.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
And behold, Elizabeth your kinswoman, even she has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who is called barren;
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
for nothing shall be impossible with God.
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
And Mary said: Behold the handmaid of the Lord; let it be to me according to your word. And the angel departed from her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
And Mary arose in those days, and went with haste into the mountainous country, into a city of Judah;
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
and she came into the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
And it came to pass, when Elizabeth heard the salutation of Mary, that the babe in her womb leaped for joy.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
And Elizabeth was filled with the Holy Spirit, and spoke with a loud voice, and said: Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
And whence is this to me, that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For, behold, when the voice of your salutation sounded in my ears, the babe in my womb leaped for joy.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
And blessed is she who believed; for there shall be a fulfillment of the things which were spoken to her from the Lord.
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
And Mary said: My soul magnifies the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
and my spirit rejoices in God, my Savior;
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
for he has looked upon the lowly condition of his handmaid. For, behold, from this time, all generations shall call me blessed;
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
for He that is Mighty has done great things for me, and holy is his name:
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
and his mercy is from generation to generation upon those who fear him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
He has done mighty deeds with his arm; he has scattered those who are proud in the understanding of their hearts.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
He has cast down the mighty from their thrones, and exalted the lowly.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent empty away.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
He has helped Israel his servant, (as he spoke to our fathers, )
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
by remembering his mercy to Abraham and to his posterity forever. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
And Mary remained with her about three months, and returned to her own house.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Now the time for Elizabeth to be delivered had fully come; and she gave birth to a son.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
And her neighbors and relatives heard that the Lord had showed great mercy to her, and they rejoiced with her.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
And it came to pass, on the eighth day, that they came to circumcise the child; and they called him by the name of his father, Zachariah.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
And his mother answered and said: Not so: but he shall be called John.
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
And they said to her: There is no one among your relatives that is called by this name.
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
And they made signs to his father, to know what he wished him to be called.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
And having asked for a writing tablet, he wrote, saying: His name is John. And they were all astonished.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
And immediately his mouth was opened, and his tongue was loosed, and he spoke, and praised God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
And fear came on all that dwelt round about them; and all these things were talked of everywhere throughout the mountainous country of Judea.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
And all that heard them, laid them up in their hearts, and said: What, then, will this child be? And the hand of the Lord was with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
And Zachariah his father was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
Blessed be the Lord God of Israel; for he has visited and redeemed his people;
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
and he has raised up for us, in the house of David his servant, a horn of salvation,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
(as he spoke by the mouth of all his holy prophets of ancient times, ) (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
salvation from our enemies, and from the hand of all that hate us,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
in order to show the mercy promised to our fathers, and to remember his holy covenant,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
the oath which he swore to Abraham our father,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
that he would grant to us, that being delivered from the hands of our enemies, we might serve him without fear,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
in holiness and righteousness before him, all our days.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
And you, child, shall be called the prophet of the Most High; for you shall go before the face of the Lord, to make ready his ways,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
by giving to his people the knowledge of salvation in the remission of their sins,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
through the tender mercies of our God; by which the dawn from on high has visited us,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
to give light to those who sit in darkness and in the shadow of death, by guiding our feet in the way of peace.
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
And the child grew and became strong in spirit; and he was in the deserts till the day of his manifestation to Israel.

< Luka 1 >