< Luka 9 >
1 Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
Ayant réuni les douze, il leur donna force et puissance sur tous, les démons et le pouvoir de guérir des maladies.
2 Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
Puis il les envoya en mission pour prêcher le Royaume de Dieu et faire des guérisons.
3 Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
Voici ce qu'il leur dit: «N'emportez rien pour la route, ni bâton, ni sac, ni pain, ni argent, n'ayez pas même deux vêtements.
4 Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
En quelque maison que vous entriez, demeurez-y, et que, ce soit de là que vous partiez.
5 Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
Quant à ceux qui ne vous recevront pas, sortez de leur ville en secouant, en témoignage contre eux, la poussière de vos pieds.»
6 Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
Ils partirent et c'est de village en village qu'ils allaient, partout évangélisant et partout guérissant.
7 Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
Le tétrarque Hérode apprit tout ce qui se passait, et il était rendu fort perplexe par ce qu'on disait de Jésus. Pour les uns, Jean était ressuscité d'entre les morts;
8 Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
pour les autres, Élie était apparu; pour ceux-ci, un des anciens prophètes était revenu à la vie.
9 Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
«J'ai fait couper la tête à Jean, disait Hérode; qui est donc cet homme dont j'entends dire de pareilles choses?» Et il était désireux de le voir.
10 Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
A leur retour, les apôtres racontèrent à Jésus tout ce qu'ils avaient fait. Il les prit avec lui et il se retira à l'écart dans une ville appelée Bethsaïda. Mais les multitudes l'apprirent et le suivirent.
11 Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
Il les accueillit en leur parlant du Royaume de Dieu et en rendant la santé à ceux qui avaient besoin d'être guéris.
12 Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
Le jour cependant commençait à baisser, et les douze, s'approchant, lui dirent: «Congédie les foules, afin qu'elles aillent dans les villages d'alentour et dans les maisons de la campagne trouver logement et nourriture; nous sommes ici dans un désert.»
13 Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
Mais Jésus leur répondit: «Donnez-leur vous-mêmes à manger.» — Nous n'avons ici, répliquèrent-ils, que cinq pains et deux poissons, à moins que nous n'allions acheter de quoi nourrir tout ce peuple!»
14 Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
Or il y avait là à peu près cinq mille hommes. Jésus dit alors à ses disciples: «Faites-les asseoir par rangées de cinquante.»
15 Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
Ainsi firent-ils; et tout le monde s'assit.
16 Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
Puis Jésus, prenant les cinq pains et les deux poissons, leva les yeux au ciel, prononça sur eux la bénédiction, les rompit et les donna aux disciples pour qu'ils les servissent à la foule.
17 Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
Tous mangèrent, tous furent rassasiés; et on emporta les morceaux qui restaient; il y en avait douze paniers.
18 Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
Comme il était un jour à prier dans un lieu solitaire, les disciples le rejoignirent et il leur fit cette question: «Parmi ces foules, qui dit-on que je suis?»
19 Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
Ils lui répondirent ainsi: «Jean-Baptiste; d'autres: Élie; d'autres encore: un des anciens prophètes revenu à la vie.» —
20 Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
«Et vous, continua-t-il, qui dites-vous que je suis?» Pierre répondit par ces mots: «Le Christ de Dieu.»
21 Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
Il leur défendit avec les plus rigoureuses recommandations de le dire à personne,
22 Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
ajoutant qu'il lui fallait, lui, le Fils de l'homme: — beaucoup souffrir; — être rejeté par les Anciens, les chefs des prêtres et les Scribes; — être mis à mort; — ressusciter le troisième jour.»
23 Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
A tous il disait: «Si quelqu'un veut venir à ma suite, qu'il renonce à lui-même, que chaque jour il porte sa croix, et qu'il me suive.
24 Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
Celui qui voudra sauver sa vie, la perdra; et il sauvera sa vie, celui qui l'aura perdue à cause de moi.
25 Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
A quoi servirait-il à un homme de gagner le monde entier, si c'est en se perdant lui-même et en consommant sa ruine?
26 Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
De celui qui aura eu honte de moi et de mes paroles, le Fils de l'homme aura honte à son tour quand il viendra dans sa gloire et dans celle du Père et des saints anges.
27 Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
Je vous dis la vérité: Quelques-uns sont ici présents qui ne goûteront point la mort, avant d'avoir vu le Royaume de Dieu.»
28 Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
Huit jours environ après avoir ainsi parlé, Jésus emmena avec lui Pierre, Jean et Jacques, et s'en alla prier sur la montagne.
29 Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
Tandis qu'il priait, l'aspect de son visage changea et ses vêtements devinrent d'une blancheur resplendissante.
30 Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
Deux hommes étaient là qui s'entretenaient avec lui; c'étaient Moïse et Élie
31 Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
apparaissant en grande gloire; ils parlaient de sa sortie du monde qu'il devait accomplir à Jérusalem.
32 Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
Cependant Pierre et ses compagnons avaient succombé au sommeil. C'est à leur réveil qu'ils virent sa gloire et les deux hommes qui se tenaient près de lui.
33 Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
Au moment où ceux-ci se séparaient de Jésus, Pierre lui dit: «Maître, qu'il nous est bon d'être ici! dressons trois tentes, une pour toi, une pour Moïse, une pour Élie!» Il ne savait ce qu'il disait.
34 Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
Pendant qu'il parlait, survint une nuée qui les enveloppa. Les disciples furent frappés de terreur quand ils les virent entrer dans la nuée.
35 Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
Or, de cette nuée sortit une voix disant: «Celui-ci est mon Fils, l'élu, écoutez-le!»
36 Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
Quand la voix se tut, Jésus se trouva seul. Ses disciples gardèrent le silence sur ce qu'ils avaient vu, et, à ce moment-là, n'en racontèrent rien à personne.
37 Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
Lorsque le lendemain ils descendirent de la montagne, une nombreuse multitude vint à la rencontre de Jésus
38 Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
et voilà que du sein de la foule un homme s'écria: «Maître, je t'en supplie, jette un regard sur mon fils; c'est mon seul enfant;
39 Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
et il y a un Esprit qui s'empare de lui: tout à coup il lui arrache un cri, lui donne des convulsions, le fait écumer et quand il se décide à le quitter, c'est pour le laisser tout brisé.
40 Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
J'ai prié tes disciples de le chasser, cela leur a été impossible.» —
41 Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
«Ô génération incrédule et perverse, dit Jésus en lui répondant, jusqu'à quand serai-je au milieu de vous et vous supporterai-je? Amène ici ton fils.»
42 Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
L'enfant s'approchait, quand le démon le jeta contre terre et lui donna des convulsions. Mais Jésus, menaçant l'Esprit impur, guérit l'enfant et le rendit à son père.
43 Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
Tous furent confondus de la grandeur de Dieu. Comme tout le monde s'émerveillait de tout ce que Jésus faisait, il dit à ses disciples:
44 “Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
«Pour vous, mettez bien dans votre mémoire les paroles que voici: «Le Fils de l'homme va être livré entre les mains des hommes.»
45 Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
Les disciples ne comprirent pas ce langage; il était voilé pour eux, afin qu'ils n'en sentissent pas la portée, et c'était un sujet sur lequel ils avaient peur de l'interroger.
46 Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
Entre eux une discussion s'éleva: lequel était le plus grand,
47 Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
Jésus, qui connaissait les pensées de leur coeur, prit un enfant, le plaça près de lui,
48 sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
et leur dit: «Qui reçoit en mon nom cet enfant-là, me reçoit; et qui me reçoit, reçoit Celui qui m'a envoyé. Car celui qui est le plus petit parmi vous tous, c'est celui-là qui est grand!»
49 Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
Jean prit la parole: «Maître, dit-il, nous avons vu un homme chasser des démons en ton nom, et nous l’en avons empêché, parce qu'il ne te suit pas avec nous.» —
50 Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
«Ne l'en empêchez point! répondit Jésus; car celui qui n'est pas contre vous est pour vous.»
51 Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
Cependant les jours où il devait être enlevé de ce monde approchaient et, d'un visage ferme, il partit pour Jérusalem,
52 Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
envoyant devant lui des messagers. Ceux-ci étant entrés, en s'en allant, dans un village de la Samarie pour lui préparer un logement,
53 Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
on refusa de le recevoir, parce que c'était vers Jérusalem qu'il tournait ses pas.
54 Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
«Seigneur, dirent les disciples présents, Jacques et Jean, veux-tu que nous disions au feu du ciel de descendre et de réduire en cendres ces gens-là!»
55 Amma, ya juya ya tsauta masu.
Jésus se tourna vers eux et les réprimanda;
56 Sai suka tafi wani kauye dabam.
et ils allèrent dans un autre village.
57 Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
Pendant qu'ils étaient en chemin, quelqu'un lui dit: «Je te suivrai partout où tu iras.»
58 Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
Jésus lui répondit: «Les renards ont des tanières et les oiseaux du ciel ont des nids; mais le Fils de l'homme n'a pas où reposer sa tête.»
59 Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
A un autre il dit: «Suis-moi.» Celui-ci lui répondit: «Permets-moi d'aller d'abord ensevelir mon père; »
60 Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
mais Jésus reprit: «Laisse les morts ensevelir leurs morts. Pour toi, va annoncer le Règne de Dieu.»
61 Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
Un autre encore lui dit: «Je te suivrai, Seigneur; mais permets-moi d'abord de prendre congé de ma famille.»
62 Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”
A celui-là Jésus répondit: «Quiconque en posant la main sur la charrue regarde en arrière, n'est pas propre au Royaume de Dieu.»