< Luka 9 >
1 Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
Then calling the Twelve together He conferred on them power and authority over all the demons and to cure diseases;
2 Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
and sent them out to proclaim the Kingdom of God and to cure the sick.
3 Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
And He commanded them, "Take nothing for your journey; neither stick nor bag nor bread nor money; and do not have an extra under garment.
4 Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
Whatever house you enter, make that your home, and from it start afresh.
5 Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
Wherever they refuse to receive you, as you leave that town shake off the very dust from your feet as a protest against them."
6 Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
So they departed and visited village after village, spreading the Good News and performing cures everywhere.
7 Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
Now Herod the Tetrarch heard of all that was going on; and he was bewildered because of its being said by some that John had come back to life,
8 Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
by others that Elijah had appeared, and by others that some one of the ancient Prophets had come back to life.
9 Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
And Herod said, "John I have beheaded; but who is this, of whom I hear such reports?" And he sought for an opportunity of seeing Jesus.
10 Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
The Apostles, on their return, related to Jesus all they had done. Then He took them and withdrew to a quiet retreat, to a town called Bethsaida.
11 Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
But the immense crowd, aware of this, followed Him; and receiving them kindly He proceeded to speak to them of the Kingdom of God, and those who needed to be restored to health, He cured.
12 Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
Now when the day began to decline, the Twelve came to Him and said, "Send the people away, that they may go to the villages and farms round about and find lodging and a supply of food; because here we are in an uninhabited district."
13 Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
"You yourselves," He said, "must give them food." "We have nothing," they replied, "but five loaves and a couple of fish, unless indeed we were to go and buy provisions for all this host of people."
14 Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
(For there were about 5,000 adult men.) But He said to His disciples, "Make them sit down in parties of about fifty each."
15 Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
They did so, making them all, without exception, sit down.
16 Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
Then He took the five loaves and the two fish, and looking up to Heaven He blessed them and broke them into portions which He gave to the disciples to distribute to the people.
17 Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
So they ate and were fully satisfied, all of them; and what they had remaining over was gathered up, twelve baskets of fragments.
18 Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
One day when He was praying by Himself the disciples were present; and He asked them, "Who do the people say that I am?"
19 Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
"John the Baptist," they replied; "but others say Elijah; and others that some one of the ancient Prophets has come back to life."
20 Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
"But you," He asked, "who do you say that I am?" "God's Anointed One," replied Peter.
21 Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
And Jesus strictly forbad them to tell this to any one;
22 Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
and He said, "The Son of Man must suffer much cruelty, be rejected by the Elders and High Priests and Scribes, and be put to death, and on the third day be raised to life again."
23 Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
And He said to all, "If any one is desirous of following me, let him ignore self and take up his cross day by day, and so be my follower.
24 Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
For whoever desires to save his life shall lose it, and whoever loses his life for my sake shall save it.
25 Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
Why, what benefit is it to a man to have gained the whole world, but to have lost or forfeited his own self.
26 Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
For whoever shall have been ashamed of me and my teachings, of him the Son of Man will be ashamed when He comes in His own and the Father's glory and in that of the holy angels.
27 Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
I tell you truly that there are some of those who stand here who will certainly not taste death till they have seen the Kingdom of God."
28 Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
It was about eight days after this that Jesus, taking with Him Peter, John, and James, went up the mountain to pray.
29 Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
And while He was praying the appearance of His face underwent a change, and His clothing became white and radiant.
30 Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
And suddenly there were two men conversing with Him, who were Moses and Elijah.
31 Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
They came in glory, and kept speaking about His death, which He was so soon to undergo in Jerusalem.
32 Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
Now Peter and the others were weighed down with sleep; but, keeping themselves awake all through, they saw His glory, and the two men standing with Him.
33 Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
And when they were preparing to depart from Him, Peter said to Jesus, "Rabbi, we are thankful to you that we are here. Let us put up three tents--one for you, one for Moses, and one for Elijah." He did not know what he was saying.
34 Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
But while he was thus speaking, there came a cloud which spread over them; and they were awe-struck when they had entered into the cloud.
35 Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
Then there came a voice from within the cloud: "This is My Son, My Chosen One: listen to Him."
36 Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
After this voice had spoken, Jesus was found alone. They kept it to themselves, and said not a word to any one at that time about what they had seen.
37 Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
On the following day, when they were come down from the mountain, a great crowd came to meet Him;
38 Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
and a man from the crowd called out, "Rabbi, I beg you to pity my son, for he is my only child.
39 Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
At times a spirit seizes him and he suddenly cries out. It convulses him, and makes him foam at the mouth, and does not leave him till it has well-nigh covered him with bruises.
40 Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
I entreated your disciples to expel the spirit, but they could not."
41 Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
"O unbelieving and perverse generation!" replied Jesus; "how long shall I be with you and bear with you? Bring your son here to me."
42 Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
Now while the youth was coming, the spirit dashed him to the ground and cruelly convulsed him. But Jesus rebuked the foul spirit, and cured the youth and gave him back to his father.
43 Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
And all were awe-struck at the mighty power of God. And while every one was expressing wonder at all that He was doing, He said to his disciples,
44 “Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
"As for you, store these my sayings in your memory; for, before long, the Son of Man will be betrayed into the hands of men."
45 Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
But they did not understand His meaning: it was veiled from them that they might not perceive it, and they were afraid to ask Him about it.
46 Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
Now there arose a dispute among them, which of them was to be the greatest.
47 Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
And Jesus, knowing the reasoning that was in their hearts, took a young child and made him stand by His side
48 sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
and said to them, "Whoever for my sake receives this little child, receives me; and whoever receives me, receives Him who sent me. For the lowliest among you all--he is the greatest."
49 Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
"Rabbi," replied John, "we have seen a man making use of your name to expel demons; and we forbad him, because he does not come with us."
50 Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
"Do not forbid him," said Jesus, "for he who is not against you is on your side."
51 Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
Now when the time drew near for Him to be received up again into Heaven, He proceeded with fixed purpose towards Jerusalem, and sent messengers before Him.
52 Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
They went and entered a village of the Samaritans to make ready for Him.
53 Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
But the people there would not receive Him, because He was evidently going to Jerusalem.
54 Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
When the disciples James and John saw this, they said, "Master, do you wish us to order fire to come down from Heaven and consume them?"
55 Amma, ya juya ya tsauta masu.
But He turned and rebuked them.
56 Sai suka tafi wani kauye dabam.
And they went to another village.
57 Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
And, as they proceeded on their way, a man came to Him and said, "I will follow you wherever you go."
58 Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
"The foxes have holes," said Jesus, "and the birds of the air have nests; but the Son of Man has nowhere to lay His head."
59 Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
"Follow me," He said to another. "Master," the man replied, "allow me first to go and bury my father."
60 Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
"Leave the dead," Jesus rejoined, "to bury their own dead; but you must go and announce far and wide the coming of the Kingdom of God."
61 Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
"Master," said yet another, "I will follow you; but allow me first to go and say good-bye to my friends at home."
62 Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”
Jesus answered him, "No one who has put his hand to the plough, and then looks behind him, is fit for the Kingdom of God.