< Luka 8 >
1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
I stało się potem, że on chodził po miastach i po miasteczkach każąc i opowiadając królestwo Boże, a oni dwunastu byli z nim,
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
I niektóre niewiasty, które był uzdrowił od duchów złych i od niemocy ich, jako Maryja, którą zwano Magdaleną, z której było siedm dyjabłów wyszło;
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
I Joanna, żona Chuzego, urzędnika Herodowego, i Zuzanna, i inszych wiele, które mu służyły z majętności swoich.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
A gdy się schodził wielki lud, i z różnych miast garnęli się do niego, rzekł przez podobieństwo;
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
Wyszedł rozsiewca, aby rozsiewał nasienie swoje; a gdy on rozsiewał, tedy jedno padło podle drogi i podeptane jest, a ptaki niebieskie podziobały je.
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
A drugie padło na opokę, a gdy wzeszło, uschło, przeto iż nie miało wilgotności.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
A drugie padło między ciernie; ale ciernie wespół z niem wzrosły, i zadusiły je.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
A drugie padło na ziemię dobrą, a gdy wzeszło, przyniosło pożytek stokrotny. To mówiąc wołał: Kto ma uszy ku słuchaniu, niechaj słucha!
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
I pytali go uczniowie jego, mówiąc: Co by to było za podobieństwo?
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
A on im rzekł: Wam dano wiedzieć tajemnicę królestwa Bożego; ale innym w podobieństwach, aby widząc nie widzieli, a słysząc nie rozumieli.
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
A to podobieństwo takie jest: nasienie jest słowo Boże.
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
A którzy podle drogi, ci są, którzy słuchają, zatem przychodzi dyjabeł, i wybiera słowo z serca ich, aby uwierzywszy, nie byli zbawieni.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
A którzy na opoce, ci są, którzy gdy słuchają, z radością słowo przyjmują, ale ci korzenia nie mają, ci do czasu wierzą, a czasu pokusy odstępują.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
A które padło między ciernie, ci są, którzy słuchają słowa: ale odszedłszy, od pieczołowania i bogactw, i rozkoszy żywota bywają zaduszeni, i nie przynoszą pożytku.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
Ale które padło na ziemię dobrą, ci są, którzy w sercu uprzejmem i dobrem słyszane słowo zachowują, i owoc przynoszą w cierpliwości.
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
A żaden zapaliwszy świecę, nie nakrywa jej naczyniem, ani jej kładzie pod łoże, ale ją stawia na świeczniku, aby ci, którzy wchodzą, widzieli światło.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
Bo nie masz nic tajemnego, co by nie miało być objawiono; i nie masz nic skrytego, czego by się nie dowiedziano, i co by na jaw nie wyszło.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
Przetoż patrzcie, jako słuchacie: albowiem kto ma, temu będzie dane, a kto nie ma, i to, co mniema, że ma, będzie odjęte od niego.
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
Tedy przyszli do niego matka i bracia jego; ale do niego przystąpić nie mogli dla ludu.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
I dano mu znać, mówiąc: Matka twoja i bracia twoi stoją przed domem, chcąc cię widzieć.
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
A on odpowiadając, rzekł do nich: Matka moja i bracia moi są ci, którzy słowa Bożego słuchają i czynią je.
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
I stało się dnia jednego, że on wstąpił w łódź i uczniowie jego, i rzekł do nich: Przeprawmy się na drugą stronę jeziora. I puścili się.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
A gdy płynęli, usnął. I przypadła nawałność wiatru na jezioro, i łódź się zalewała, tak że byli w niebezpieczeństwie.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
A przystąpiwszy, obudzili go, mówiąc: Mistrzu, mistrzu! giniemy. A on ocknąwszy się, zgromił wiatr i wały wodne, i uśmierzyły się, i stało się uciszenie.
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
Tedy im rzekł: Gdzież jest wiara wasza? A bojąc się, dziwowali się, mówiąc jedni do drugich: Któż wżdy jest ten, że i wiatrom rozkazuje i wodom, a są mu posłuszne?
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
I przewieźli się do krainy Gadareńczyków, która jest przeciw Galilei.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
A gdy wstąpił na ziemię, zabieżał mu mąż niektóry z onego miasta, co miał dyjabły od niemałego czasu, a nie obłóczył się w szaty, i nie mieszkał w domu, tylko w grobach.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
Ten ujrzawszy Jezusa, zakrzyknął, i upadł przed nim, a głosem wielkim rzekł: Cóż ja mam z tobą, Jezusie, Synu Boga najwyższego? proszę cię, nie dręcz mię.
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
Albowiem rozkazał onemu duchowi nieczystemu, aby wyszedł z onego człowieka: bo od wielu czasów porywał go; a chociaż go wiązano łańcuchami i w pętach strzeżono, jednak on porwawszy okowy, bywał od dyjabła na pustynię pędzony.
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
I pytał go Jezus, mówiąc: Co masz za imię? A on rzekł: Wojsko; albowiem wiele dyjabłów wstąpiło było weń.
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos )
Tedy go prosili, aby im nie rozkazywał stamtąd odejść w przepaść. (Abyssos )
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
A była tam trzoda wielka świń, która się pasła na górze, i prosili go, aby im dopuścił wstąpić w nie. I dopuścił im.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
A wyszedłszy dyjabli z onego człowieka, weszli w świnie; i porwała się ona trzoda pędem z przykra do jeziora, i utonęła.
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
A widząc pasterze, co się stało, uciekli; a poszedłszy, oznajmili to w mieście i we wsiach.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
I wyszli, aby oglądali to, co się stało; a przyszedłszy do Jezusa, znaleźli człowieka onego, z którego wyszli dyjabli, obleczonego, przy dobrem baczeniu, siedzącego u nóg Jezusowych, i bali się.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
Opowiedzieli im tedy ci, którzy widzieli, jako uzdrowiono tego, który był opętany.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
I prosiło go wszystko mnóstwo onej okolicznej krainy Gadareńczyków, aby odszedł od nich; albowiem ich był wielki strach ogarnął. A on wstąpiwszy w łódź, wrócił się.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
I prosił go on mąż, z którego wyszli dyjabli, aby był przy nim; ale go Jezus odprawił, mówiąc:
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
Wróć się do domu twego, a opowiadaj, jakoć wielkie rzeczy Bóg uczynił. I odszedł, po wszystkiem mieście opowiadając, jako mu wielkie rzeczy Jezus uczynił.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
I stało się, gdy się wrócił Jezus, że go przyjął lud; albowiem nań wszyscy oczekiwali.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
A oto przyszedł mąż imieniem Jairus, a ten był przełożonym bóżnicy; a przypadłszy do nóg Jezusowych, prosił go, aby wszedł w dom jego.
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
Albowiem miał córkę jedyną około dwunastu lat, która już konała. (A gdy on szedł, cisnął go lud.)
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
A niewiasta, która płynienie krwi cierpiała od lat dwunastu, i wynałożyła była na lekarzy wszystko swoje pożywienie, a nie mogła być od nikogo uleczona,
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
Przystąpiwszy z tyłu, dotknęła się podołka szaty jego, a zarazem się zastanowiło płynienie krwi jej.
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
I rzekł Jezus: Któż jest, co się mnie dotknął? a gdy się wszyscy zapierali, rzekł Piotr, i ci, którzy z nim byli: Mistrzu! lud cię ciśnie i tłoczy, a ty mówisz: Kto się mnie dotknął?
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
I rzekł Jezus: Dotknął się mnie ktoś, bom poznał, że moc ode mnie wyszła.
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
A widząc ona niewiasta, że się nie utaiła, ze drżeniem przystąpiła i upadła przed nim, i dlaczego się go dotknęła, powiedziała mu przed wszystkim ludem, i jako zaraz uzdrowiona była.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
A on jej rzekł: Ufaj, córko! wiara twoja ciebie uzdrowiła; idźże w pokoju.
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
A gdy on to jeszcze mówił, przyszedł niektóry od przełożonego bóżnicy, powiadając mu: Iż umarła córka twoja, nie trudź Nauczyciela.
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
Ale Jezus usłyszawszy to, odpowiedział mu, mówiąc: Nie bój się, tylko wierz, a będzie uzdrowiona.
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
A wszedłszy w dom, nie dopuścił z sobą wnijść nikomu, tylko Piotrowi, i Jakóbowi, i Janowi, i ojcu i matce onej dzieweczki.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
A płakali wszyscy, i narzekali nad nią. Ale on rzekł: Nie płaczcież! Nie umarłać, ale śpi.
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
I naśmiewali się z niego, wiedząc, iż była umarła.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
A on wygnawszy precz wszystkich, i ująwszy ją za rękę, zawołał, mówiąc: Dzieweczko, wstań!
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
I wrócił się duch jej; i wstała zaraz; i rozkazał, aby jej jeść dano.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
I zdumieli się rodzice jej. A on im zakazał, aby nikomu nie powiadali tego, co się było stało.