< Luka 8 >

1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
And it came to pass consecutively, that He was going through city and village, proclaiming and preaching the gospel of God, and the twelve along with Him.
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
And certain women who had been healed of evil spirits and infirmities, Mary called Magdalene, from whom seven demons had gone out,
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
and Joanna the wife of Chuzas the steward of Herod, and Susanna, and many other women, who were accustomed to minister unto Him from those things belonging to them.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
A great multitude being with Him, and coming to Him throughout every city, He spoke in a parable:
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
A sower went out to sow his seed. And while he was sowing, some fell by the way, and was trodden under foot, and the birds of the air devoured it.
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
And other fell on the rock; and springing up, withered away, because it had no moisture.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
And other fell in the midst of thorns, and the thorns growing together, choked it out.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
And other fell into good ground, and springing up, produced fruit, a hundredfold. Speaking these things, He cried out, Let the one having ears to hear, hear.
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
And His disciples asked Him saying, What might this parable be?
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
And He said; To you it has been given to know the mysteries of the kingdom of God: but to the rest in parables; in order that seeing they may not see, and hearing they may not understand.
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
And this is the parable: The seed is the word of God.
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
And there are those who hear by the wayside; then the devil comes, and takes away the word from their heart, lest they believing may be saved.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
And those on the stones are they who, when they may hear, receive the word with joy; and they have no root in them, who believe for a time, and in time of temptation they fall away.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
And that which falleth among thorns, there are those who hear, and going forward, by the cares and riches and pleasures are choked out, and bring forth no fruit to perfection.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
And that which is in the good ground, are those whosoever hearing the word in a beautiful and good heart, retain it, and bring forth fruit with patience.
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
But no one having lighted a candle covers it with a vessel, or puts it under a bed; but he places it on a candlestick, in order that those coming in may see the light.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
For there is nothing hidden which shall not be made manifest; neither is there any thing concealed, which may not be made known and come into the light.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
Therefore see how you hear: for whosoever may have, it shall be given unto him; and whosoever may not have, it shall be taken from him, even that which he seems to have.
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
And His mother and His brothers came to Him, and were not able to reach Him on account of the crowd.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
And it was told Him, Thy mother and thy brothers stand without, wishing to see thee.
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
And He responding said to them, My mother and my brothers are the ones hearing the word of God, and doing it.
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
And it came to pass on one of the days, He and His disciples went into a ship. And He said to them, Let us go to the other side of the lake. And they were embarked.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
And they sailing, He was asleep: and a storm of wind came down into the lake; and they were being filled, and imperiled.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
And they having come to Him, awakened Him, saying, Master, Master, we perish. And He having arisen, rebuked the wind and the wave of the water: and they ceased, and there was a calm.
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
And He said to them, Where is your faith? And they being afraid were astonished, saying to one another, Who then is this, because He commands the winds and the water, and they obey Him?
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
And they sailed into the country of the Gergesenes, which is over against Galilee.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
And a certain man from the city, who a long time had demons, and did not wear clothing, and did not remain in the house, but in the tombs; met Him having come to the land.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
And seeing Jesus, and crying out, he worshiped Him, and said with a loud voice; What is there to me and to thee, O Jesus, Son of the Most High God? I pray thee torment me not.
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
For He commanded the unclean spirit to come out from the man; for since a long time he had possessed him, and he was frequently bound, secured with chains and fetters, and smashing his bonds, was driven by the demons into the desert.
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
And Jesus asked him saying, What is thy name? And he said Legion; because many demons entered into him.
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
And he continued to intreat Him that He should not command them to depart into the abyss. (Abyssos g12)
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
And there was a herd of many swine feeding in the mountain: and they continued to intreat Him that He should permit them to go into them. And He permitted them.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
And the demons having come out from the man, came into the swine: and the herd rushed down a precipice into the sea, and were strangled.
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
And the herders seeing that which took place, fled, and proclaimed it in the city and in the country.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
And they came out to see that which had happened; and came to Jesus, and found the man, out of whom the demons had gone, clothed and in his right mind, at the feet of Jesus: and they were afraid.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
And those seeing reported to them how the demonized man was saved.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
And all the multitudes of the surrounding country of the Gergesenes, asked Him to depart from them; because they were seized with great fear. And He having come Into the ship, returned.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
And the man out of whom the demons had gone prayed to be with Him. And Jesus sent him away, saying,
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
Return to thy own house, and relate, how many things God has done unto thee. And he departed throughout the whole city, preaching how many things Jesus did unto him.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
And it came to pass when Jesus returned, the multitude received Him; for they were all looking for Him.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
Behold, a man to whom was the name Jairus, and he was a ruler of the synagogue: and falling at the feet of Jesus, he continued to intreat Him to come into his house;
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
for there was an only daughter to him, of twelve years, and she was dying. And while He was going the multitudes were thronging Him.
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
And a woman being in an issue of blood twelve years, who having expended all her living with physicians, was not able to be healed by any of them,
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
and having come to Him behind, she touched the hem of His garment: and immediately the issue of blood ceased.
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
And Jesus said, Who is the one having touched me? And all denying, Peter and the disciples with Him said, The multitudes crowd thee and press upon thee, and dost thou say, Who is the one having touched me?
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
And Jesus said, Some one touched me: for I know the power went out from me.
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
And the woman seeing that she was not concealed, came trembling, and falling down before Him, proclaimed on account of what cause she touched Him, in the presence of all the people, and how she was healed immediately.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
And He said to her, Be of good cheer, daughter; thy faith hath saved thee; go in peace.
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
And He yet speaking, a certain one comes from the house of the chief ruler of the synagogue, saying to him, Thy daughter is dead; trouble not the Teacher:
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
and Jesus hearing, responded to him, saying, Fear not: only believe, and she shall be saved.
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
And having come to the house, He did not suffer any to enter except Peter, John, and James, and the father and mother of the child.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
And they were all weeping, and wailing over her: and He said, Weep not; she is not dead, but sleepeth.
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
And they hooted at Him, knowing that she was dead.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
And having put all out, taking her by the hand, He spoke, saying, Child, arise.
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
And her spirit returned, and she stood up immediately. And He commanded that something should be given to her to eat.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
And her parents were delighted: and He commanded them to tell no one that which had taken place.

< Luka 8 >