< Luka 8 >
1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
Now it happened after this that He started going around town by town, village by village, preaching and proclaiming the good news of the Kingdom of God, and the twelve were with Him;
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
also certain women who had been healed of malignant spirits and infirmities: Mary (the one called Magdalene) from whom seven demons had gone out;
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
and Joanna the wife of Chuza, an official of Herod; and Susanna, and many others—these were providing for Him from their substance.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
Now when a large crowd had gathered, with people coming to Him from town after town, He spoke by a parable:
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
“A sower went out to sow his seed; and as he sowed some fell along the road, and it got trampled, and the birds of the air devoured it.
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
And some fell on the rock ledge, and upon sprouting it withered, because it had no moisture.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
And some fell among thorns, and springing up together the thorns choked it.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
The rest fell into the good ground, and growing up it produced fruit a hundredfold.” Upon saying these things He called out, “He who has ears to hear, let him hear!”
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
Then His disciples asked Him saying, “What does this parable mean?”
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
So He said: “To you it has been given to know the mysteries of the Kingdom of God, but to the rest only in parables, so that ‘seeing they may not see, and hearing they may not understand.’
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
“Now here is the parable: The seed is the Word of God.
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
Those along the road are those who hear; then the devil comes and takes away the word from their hearts, in order that they not be saved, having believed.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
Those on the rock ledge are the ones who, whenever they hear, receive the word with joy; yet these have no root, who believe for a while and in time of testing fall away.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
Now that which fell into the thorns: these are the ones who heard, yet as they go they are choked by cares, riches, and pleasures of life, and bring no fruit to maturity.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
But that on the good ground: these are the ones who having heard the word with a noble and good heart, hold on to it and produce fruit with perseverance.”
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
Upon saying these things He called out: “He who has ears to hear, let him hear! No one, when he has lit a lamp, covers it with a vessel or puts it under a bed, but he sets it on a lamp stand, so that those who come in may see the light.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
Further, there is nothing hidden that will not be revealed, nor anything concealed that will not be made known and come into the open.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
So be careful how you hear: Because whoever has, to him more will be given; and whoever does not have, even what he thinks he has will be taken away from him.”
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
Then His mother and brothers came to Him, and they could not get near Him because of the crowd.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
And it was told Him by some saying, “Your mother and your brothers are standing outside, wanting to see you.”
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
But in answer He said to them, “My mother and my brothers are these, the ones who hear the word of God and do it!”
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
Now it happened on one of those days that He got into a boat with His disciples; and He said to them, “Let us go over to the other side of the lake.” So they launched out.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
But as they sailed He fell asleep. A windstorm descended on the lake, and they were being swamped and were in jeopardy.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
So they came and awakened Him, saying, “Master, Master, we are perishing!” Then He got up and rebuked the wind and the waves of water—and they stopped, and there was a calm!
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
So He said to them, “Where is your faith?” But being terrified they marveled, saying to each other: “Who can this be? Because He commands even the winds and the water, and they obey Him!”
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
Then they sailed to the district of the Gadarenes, which is opposite Galilee.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
Well when He stepped out on the land, a certain man of that town met Him, who had had demons for a long time—he wore no clothes, nor did he live in a house, but among the tombs.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
When he saw Jesus he gave a yell, fell down before Him, and with a loud voice he said: “What do you want with me, Jesus, Son of the Most High God? I beg you, don't torment me!”
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
because He had commanded the unclean spirit to get out of the man (it had seized him many times—he would be bound with chains and shackles, being kept under guard; then bursting the bonds he would be driven by the demon into deserted places).
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
Then Jesus asked him, “What is your name?” And he said, “Legion” (because many demons had gone into him).
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos )
And he kept imploring Him that He would not order them to go away into the Abyss. (Abyssos )
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
Now a herd of many pigs was feeding there on the hillside; and they started begging Him that He would allow them to go into those; so He gave them permission.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
Then the demons exited the man and entered the pigs—and the herd rushed down the steep bank into the lake and was drowned!
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
Well when the herders saw what had happened they ran away and reported it in the town and in the countryside.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
So they went out to see what had happened, and came to Jesus; they found the man from whom the demons had gone out sitting at Jesus' feet, clothed and in his right mind; and they were afraid.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
Also, the eyewitnesses reported to them how the demonized man was healed.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
Then the whole multitude from the surrounding region of the Gadarenes asked Him to depart from them, because they were overcome by fear. So He got into the boat and returned.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
Now the man from whom the demons had gone out had started begging Him that he might be with Him. But Jesus sent him away, saying,
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
“Return to your house and recount how much God has done for you.” So he went his way and proclaimed all over town how much Jesus had done for him.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
Now it happened, when Jesus returned, that the crowd welcomed Him, because they were all waiting for Him.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
And then, there came a man named Jairus, and he was a ruler of the synagogue; he fell down at Jesus' feet and started begging Him to come to his house,
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
because he had an only daughter, about twelve years old, and she was dying. Now as He was going, the crowds were pressing against Him.
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
And a woman—suffering with a flow of blood for twelve years, who had spent her whole livelihood on physicians, but could not be healed by any—
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
approaching from behind touched the border of His garment; and immediately the flow of her blood stopped!
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
So Jesus said, “Who touched me?” When all denied it, Peter and those with him said: “Master, the people are pressing against you and crowding in, and you say, ‘Who touched me?’”
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
But Jesus said, “Someone did touch me, because I noticed power going out from me.”
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
Now when the woman saw that she could not hide, she came trembling, and falling down before Him she told Him in the presence of all the people the reason why she had touched Him, and how she was healed immediately.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
So He said: “Courage, daughter, your faith has healed you. Go into peace.”
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
While He was still speaking, here came someone from the synagogue ruler's house, saying to him: “Your daughter has died. Don't bother the teacher.”
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
But upon hearing it Jesus reacted by saying to him, “Don't be afraid; just believe and she will be healed.”
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
When He arrived at the house, He allowed no one to go in except Peter, John, James, the father of the child, and her mother.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
Now all were weeping and mourning for her; but He said, “Do not weep; she is not dead, but sleeping.”
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
They started ridiculing Him, knowing that she had died.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
So He put them all outside, and grasping her hand He called, saying, “Child, arise!”
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
Then her spirit returned, and she got right up! And He directed that she be given something to eat.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
Her parents were astonished, but He charged them to tell no one what had happened.