< Luka 7 >
1 Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
After He had finished teaching all these things in the hearing of the people, He went into Capernaum.
2 Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
Here the servant of a certain Captain, a man dear to his master, was ill and at the point of death;
3 Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
and the Captain, hearing about Jesus, sent to Him some of the Jewish Elders, begging Him to come and restore his servant to health.
4 Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
And they, when they came to Jesus, earnestly entreated Him, pleading, "He deserves to have this favour granted him,
5 saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
for he loves our nation, and at his own expense he built our synagogue for us."
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
Then Jesus went with them. But when He was not far from the house, the Captain sent friends to Him with the message: "Sir, do not trouble to come. I am not worthy of having you come under my roof;
7 Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
and therefore I did not deem myself worthy to come to you. Only speak the word, and let my young man be cured.
8 Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
For I too am a man obedient to authority, and have soldiers under me; and I say to one, 'Go,' and he goes; to another, 'Come,' and he comes; and to my slave, 'Do this or that,' and he does it."
9 Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
Jesus listened to the Captain's message and was astonished at him, and He turned and said to the crowd that followed Him, "I tell you that not even in Israel have I found faith like that."
10 Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
And the friends who had been sent, on returning to the house, found the servant in perfect health.
11 Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
Shortly afterwards He went to a town called Nain, attended by His disciples and a great crowd of people.
12 Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
And just as He reached the gate of the town, they happened to be bringing out for burial a dead man who was his mother's only son; and she was a widow; and a great number of the townspeople were with her.
13 Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
The Lord saw her, was moved with pity for her, and said to her, "Do not weep."
14 Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
Then He went close and touched the bier, and the bearers halted. "Young man," He said, "I command you, wake!"
15 Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
The dead man sat up and began to speak; and He restored him to his mother.
16 Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
All were awe-struck, and they gave glory to God--some saying, "A Prophet, a great Prophet, has risen up among us." Others said, "God has not forgotten His People."
17 Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
And the report of what Jesus had done spread through the whole of Judaea and in all the surrounding districts.
18 Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
John's disciples brought him an account of all these things;
19 Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
so John called two of his disciples and sent them to the Lord. "Are you the Coming One?" he asked, "or is there another that we are to expect?"
20 Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
The men came to Jesus and said, "John the Baptist has sent us to you with this question: 'Are you the Coming One, or is there another that we are to expect?'"
21 A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
He immediately cured many of diseases, severe pain, and evil spirits, and to many who were blind He gave the gift of sight.
22 Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
Then He answered the messengers, "Go and report to John what you have seen and heard. Blind men receive sight, the lame walk, lepers are purified, deaf persons hear, the dead are raised to life, the poor have the Good News proclaimed to them.
23 Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
And blessed is every one who does not stumble and fall because of my claims."
24 Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
When John's messengers were gone, He proceeded to say to the multitude concerning John, "What did you go out into the Desert to gaze at? A reed waving in the wind?
25 Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
But what did you go out to see? A man wearing luxurious clothes? People who are gorgeously dressed and live in luxury are found in palaces.
26 Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
But what did you go out to see? A Prophet? Aye, I tell you, and far more than a Prophet.
27 Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
John is the man about whom it is written, 'See, I am sending My messenger before thy face, and he shall make ready thy way before thee.'
28 Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
"I tell you that among all of women born there is not one greater than John. Yet one who is of lower rank in the Kingdom of God is greater than he.
29 Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
And all the people, including the tax-gatherers, when they listened to him upheld the righteousness of God, by being baptized with John's baptism.
30 Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
But the Pharisees and expounders of the Law have frustrated God's purpose as to their own lives, by refusing to be baptized.
31 Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
"To what then shall I compare the men of the present generation, and what do they resemble?
32 Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
They are like children sitting in the public square and calling out to one another, 'We have played the flute to you, and you have not danced: we have sung dirges, and you have not shown sorrow.'
33 Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
For John the Baptist has come eating no bread and drinking no wine, and you say, 'He has a demon!'
34 Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
The Son of Man has come eating and drinking, and you say, 'Look, there is a man who is overfond of eating and drinking--he is a friend of tax-gatherers and notorious sinners!'
35 Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
But wisdom is justified by all who are truly wise."
36 Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
Now one of the Pharisees repeatedly invited Him to a meal at his house; so He entered the house and reclined at the table.
37 Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
And there was a woman in the town who was a notorious sinner. Having learnt that Jesus was at table in the Pharisee's house she brought a flask of perfume,
38 Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
and, standing behind close to His feet, weeping, began to wet His feet with her tears; and with her hair she wiped the tears away again, while she lovingly kissed His feet and poured the perfume over them.
39 Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
Noticing this, the Pharisee, His host, said to himself, "This man, if he were really a Prophet, would know who and what sort of person this woman is who is touching him--and would know that she is an immoral woman."
40 Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
In answer to his thoughts Jesus said to him, "Simon, I have a word to say to you." "Rabbi, say on," he replied.
41 Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
"There were once two men in debt to one money-lender," said Jesus; "one owed him five hundred shillings and the other fifty.
42 Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
But neither of them could pay anything; so he freely forgave them both. Tell me, then, which of them will love him most?"
43 Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
"I suppose," replied Simon, "the one to whom he forgave most." "You have judged rightly," Jesus rejoined.
44 Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
Then turning towards the woman He said to Simon, "Do you see this woman? I came into your house: you gave me no water for my feet; but she has made my feet wet with her tears, and then wiped the tears away with her hair.
45 Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
No kiss did you give me; but she from the moment I came in has not left off tenderly kissing my feet.
46 Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
No oil did you pour even on my head; but she has poured perfume upon my feet.
47 Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
This is the reason why I tell you that her sins, her many sins, are forgiven--because she has loved much; but he who is forgiven little, loves little."
48 Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
And He said to her, "Your sins are forgiven."
49 Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
Then the other guests began to say to themselves, "Who can this man be who even forgives sins?"
50 Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”
But He said to the woman, "Your faith has cured you: go, and be at peace."