< Luka 6 >

1 Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
Il arriva — un jour de sabbat — que Jésus passa par des blés; ses disciples cueillaient les épis et, les froissant dans leurs mains, en mangeaient les grains.
2 Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
«Pourquoi faites-vous, dirent quelques-uns des Pharisiens, ce qu'au jour du sabbat il n'est pas permis de faire?»
3 Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
Jésus leur répondit par ces paroles: «N'avez-vous pas lu ce que fit David quand il eut faim et ce que firent ses compagnons?
4 Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
Comment il entra dans la maison de Dieu, prit les pains de proposition, en mangea et en donna à ceux qui étaient avec lui, quand il n'est permis qu'aux prêtres seuls d'en manger?» —
5 Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
«Le Fils de l'homme, ajouta-t-il, est maître aussi du sabbat.»
6 Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
Un autre jour de sabbat, il entra dans la synagogue et il y enseigna. Il s'y trouvait un homme dont la main droite était paralysée.
7 Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
Les Scribes et les Pharisiens l'observaient pour voir si, un jour de sabbat, il le guérirait, et pour tirer de là quelque prétexte à accusation.
8 Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
Quant à lui, il connaissait leurs pensées. «Lève-toi, dit-il, à l'homme dont la main était paralysée, et tiens-toi debout au milieu de nous tous! L'homme se leva et se tint debout.
9 Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
«Je vous le demande, leur dit alors Jésus, est-il permis aux jours de sabbat de faire le bien ou de faire le mal? de sauver une vie ou de la perdre?»
10 Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
Ayant sur eux tous promené son regard, il dit à l'homme: «Étends ta main.»
11 Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
Il le fit et sa main fut guérie. Quant à eux, ils étaient fous de rage, et ils parlaient entre eux de ce qu'ils pourraient bien faire à Jésus.
12 Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
En ces jours-là, il se retira sur la montagne pour prier et passa la nuit à prier Dieu.
13 Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
Quand il fit jour, il convoqua ses disciples; et il choisit douze d'entre eux, auxquels il donna le nom d'apôtres;
14 Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
ce furent Simon, qu'il nomma Pierre, et André son frère; — Jacques et Jean; — Philippe et Barthélemi; —
15 Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
Matthieu et Thomas; — Jacques, fils d'Alphée, et Simon (celui qu'on appelle le zélateur);
16 da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
Judas, frère de Jacques, et Judas l'Iskariôte, qui fut un traître.
17 Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
Descendant de la montagne, avec eux, il s'arrêta sur un terrain uni. Là se trouvait, avec une foule considérable de ses disciples, une multitude immense de peuple, venue pour l'entendre et se faire guérir de ses maux, de toute la Judée, de Jérusalem et du littoral de Tyr et de Sidon.
18 Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
Ceux qui étaient tourmentés par des Esprits impurs en étaient délivrés
19 Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
et chacun dans la foule cherchait à le toucher, parce qu'il sortait de lui une vertu qui les guérissait tous.
20 Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
Jésus, levant les yeux sur ses disciples, dit: «Heureux êtes-vous, ô pauvres, parce qu'à vous appartient le Royaume de Dieu!»
21 Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
«Heureux, ô vous qui avez faim maintenant, parce que vous serez rassasiés!» «Heureux, ô vous qui pleurez maintenant, parce que vous rirez!»
22 Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
«Heureux serez-vous lorsque les hommes vous haïront, vous réprouveront, vous outrageront, proscriront votre nom comme maudit à cause du Fils de l’homme!
23 Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
En ce jour-là réjouissez-vous et sautez de joie! parce que votre récompense sera grande dans le ciel; car c'est de même façon que leurs pères traitaient les prophètes.»
24 Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
«Malheur à vous cependant, riches, parce que vous avez aujourd'hui votre consolation!»
25 Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
«Malheur à vous qui maintenant avez tout à satiété, parce que vous aurez faim!» «Malheur à vous qui maintenant riez, parce que vous tomberez dans le deuil et les larmes!»
26 Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
«Malheur! lorsque tous les hommes diront du bien de vous, car c'est de même façon que leurs pères traitaient les faux prophètes!»
27 Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
«Quant à vous qui m'écoutez, voici ce que je vous dis: Aimez vos ennemis; faites du bien à ceux qui vous haïssent;
28 Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
bénissez ceux qui vous maudissent; priez pour ceux qui vous font injure.
29 Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
Si quelqu'un te frappe sur une joue, présente-lui aussi l'autre; et contre celui qui t'enlève ton manteau ne défends pas même ta tunique.»
30 Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
«A qui te demande, donne; et à qui s'empare de ce qui est à toi, ne réclame rien.»
31 Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
«Comme vous voulez que les hommes agissent envers vous, agissez vous-mêmes pareillement envers eux.
32 Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
Si vous aimez ceux qui vous aiment, quel gré vous en saura-t-on? les pécheurs aussi aiment ceux qui les aiment.
33 Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
Et si vous faites du bien à ceux qui vous en font à vous-mêmes, quel gré vous en saura-t-on? Les pécheurs le font aussi.
34 Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
Et si vous prêtez à ceux dont vous espérez recevoir quelque chose, quel gré vous en saura-t-on? Les pécheurs aussi font des prêts aux pécheurs pour recevoir un jour le même service.
35 Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
Vous cependant aimez vos ennemis; faites du bien et prêtez sans espérer quoi que ce soit. Et votre récompense sera grande et vous serez fils du Très-Haut, parce qu'il est bon pour les ingrats et pour les méchants.»
36 Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
«Soyez miséricordieux, comme votre Père est miséricordieux.
37 Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
Ne jugez point et vous ne serez point jugés; ne condamnez point et vous ne serez point condamnés. Pardonnez, et il vous sera pardonné.
38 Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
Donnez, et il vous sera donné; il sera versé dans votre sein une bonne mesure, pressée, tassée, débordante, car la mesure que vous faites aux autres sera votre mesure.»
39 Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
Il leur dit aussi une parabole: «Un aveugle peut-il conduire un aveugle? Ne tomberont-ils pas tous deux dans une fosse?»
40 Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
«Le disciple n'est pas au-dessus du maître; il sera parfait quand il sera pareil à son maître.»
41 Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
«Pourquoi regardes-tu la paille qui est dans l'oeil de ton frère? Et la poutre qui est dans ton oeil à toi, tu ne la remarques pas!
42 Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
Comment peux-tu dire à ton frère: «Mon frère, laisse-moi ôter cette paille qui est dans ton oeil», ne voyant pas toi-même la poutre qui est dans le tien? Hypocrite, ôte d'abord de ton oeil la poutre et alors tu verras à ôter la paille de l'oeil de ton frère!»
43 Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
«Un arbre qui produit de mauvais fruits n'est pas bon; à l'inverse, un arbre qui produit de bons fruits n'est pas mauvais;
44 Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
car c'est par son fruit que chaque arbre se fait connaître. Sur des épines on ne cueille pas de figues; sur des ronces on ne vendange pas de raisin.»
45 Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
«Du bon trésor de son coeur l'homme bon tire le bien; de son mauvais trésor l'homme mauvais tire le mal; car c'est de l'abondance du coeur que la bouche parle.»
46 Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
«Pourquoi m'appelez-vous: «Seigneur! Seigneur!» et ne faites-vous pas ce que je dis?
47 Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
Quiconque vient à moi, entendant mes paroles et les mettant en pratique, je vais vous montrer à qui il ressemble.
48 Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
Il ressemble à un homme qui, en construisant une maison, a creusé très avant et a établi ses fondations sur le roc. L'inondation est survenue; le torrent a fait irruption sur cette maison et il n'a pas eu la force de l'ébranler, parce qu'elle était bien construite.»
49 Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
«Quant à celui qui entend et ne met pas en pratique, il ressemble à un homme qui a bâti sa maison sur la terre sans fondations. Sur elle le torrent a fait irruption; soudain elle s'est écroulée; et la ruine de cette maison a été grande.

< Luka 6 >