< Luka 6 >
1 Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
Now on the second-first Sabbath while He was passing through the wheatfields, His disciples were plucking the ears and rubbing them with their hands to eat the grain.
2 Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
And some of the Pharisees asked, "Why are you doing what the Law forbids on the Sabbath?"
3 Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
"Have you never read so much as this," answered Jesus--"what David did when he and his followers were hungry;
4 Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
how he entered the house of God and took and ate the Presented Loaves and gave some to his followers--loaves which none but the Priests are allowed to eat?"
5 Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
"The Son of Man," He added, "is Lord of the Sabbath also."
6 Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
On another Sabbath He had gone to the synagogue and was teaching there; and in the congregation was a man whose right arm was withered.
7 Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
The Scribes and the Pharisees were on the watch to see whether He would cure him on the Sabbath that they might be able to bring an accusation against Him.
8 Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
He knew their thoughts, and said to the man with the withered arm, "Rise, and stand there in the middle." And he rose and stood there.
9 Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
Then Jesus said to them, "I put it to you all whether we are allowed to do good on the Sabbath, or to do evil; to save a life, or to destroy it."
10 Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
And looking round upon them all He said to the man, "Stretch out your arm." He did so, and the arm was restored.
11 Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
But they were filled with madness, and began to discuss with one another what they should do to Jesus.
12 Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
About that time He went out on one occasion into the hill country to pray; and He remained all night in prayer to God.
13 Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
When it was day, He called His disciples; and He selected from among them twelve, whom He also named Apostles.
14 Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
These were Simon, to whom also He had given the name of Peter, and Andrew his brother; James and John; Philip and Bartholomew;
15 Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
Matthew and Thomas; James the son of Alphaeus and Simon called the Zealot;
16 da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
James's relative Judas, and Judas Iscariot who proved to be a traitor.
17 Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
With these He came down till He reached a level place, where there was a great crowd of His disciples, and a multitude of people from every part of Judaea, from Jerusalem, and from the sea-side district of Tyre and Sidon, who came to hear Him and to be cured of their diseases;
18 Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
and those who were tormented by foul spirits were cured.
19 Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
The whole crowd were eager to touch Him, because power went forth from him and cured every one.
20 Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
Then fixing His eyes upon His disciples, Jesus said to them, "Blessed are you poor, because the Kingdom of God is yours.
21 Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
"Blessed are you who hunger now, because your hunger shall be satisfied. "Blessed are you who now weep aloud, because you shall laugh.
22 Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
"Blessed are you when men shall hate you and exclude you from their society and insult you, and spurn your very names as evil things, for the Son of Man's sake.
23 Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
"Be glad at such a time, and dance for joy; for your reward is great in Heaven; for that is just the way their forefathers behaved to the Prophets!
24 Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
"But alas for you rich men, because you already have your consolation!
25 Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
"Alas for you who now have plenty to eat, because you will be hungry! "Alas for you who laugh now, because you will mourn and weep aloud!
26 Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
"Alas for you when men shall all have spoken well of you; for that is just the way their forefathers behaved to the false Prophets!
27 Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
"But to you who are listening to me I say, Love your enemies; seek the welfare of those who hate you;
28 Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
bless those who curse you; pray for those who revile you.
29 Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
To him who gives you a blow on one side of the face offer the other side also; and to him who is robbing you of your outer garment refuse not the under one also.
30 Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
To every one who asks, give; and from him who takes away your property, do not demand it back.
31 Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
And behave to your fellow men just as you would have them behave to you.
32 Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
"If you love those who love you, what credit is it to you? Why, even bad men love those who love them.
33 Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
And if you are kind to those who are kind to you, what credit is it to you? Even bad men act thus.
34 Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
And if you lend to those from whom you hope to receive, what credit is it to you? Even bad men lend to their fellows so as to receive back an equal amount.
35 Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
Nevertheless love your enemies, be beneficent; and lend without hoping for any repayment. Then your recompense shall be great, and you will be sons of the Most High; for He is kind to the ungrateful and wicked.
36 Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
Be compassionate just as your Father is compassionate.
37 Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
"Judge not, and you shall not be judged; condemn not, and you shall not be condemned; pardon, and you shall be pardoned;
38 Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
give, and gifts shall be bestowed on you. Full measure, pressed, shaken down, and running over, shall they pour into your laps; for with the same measure that you use they shall measure to you in return."
39 Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
He also spoke to them in figurative language. "Can a blind man lead a blind man?" He asked; "would not both fall into the ditch?
40 Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
There is no disciple who is superior to his teacher; but every one whose instruction is complete will be like his teacher.
41 Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
"And why look at the splinter in your brother's eye instead of giving careful attention to the beam in your own?
42 Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
How can you say to your brother, 'Brother, let me take that splinter out of your eye,' when all the while you yourself do not see the beam in your own eye? Vain pretender! take the beam out of your own eye first, and then you will see clearly to take the splinter out of your brother's eye.
43 Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
"There is no good tree that yields unsound fruit, nor again any unsound tree that yields good fruit.
44 Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
Every tree is known by its own fruit. It is not from thorns that men gather figs, nor from the bramble that they can get a bunch of grapes.
45 Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
A good man from the good stored up in his heart brings out what is good; and an evil man from the evil stored up brings out what is evil; for from the overflow of his heart his mouth speaks.
46 Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
"And why do you all call me 'Master, Master' and yet not do what I tell you?
47 Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
Every one who comes to me and listens to my words and puts them in practice, I will show you whom he is like.
48 Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
He is like a man building a house, who digs and goes deep, and lays the foundation on the rock; and when a flood comes, the torrent bursts upon that house, but is unable to shake it, because it is securely built.
49 Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
But he who has heard and not practised is like a man who has built a house upon the soft soil without a foundation, against which the torrent bursts, and immediately it collapses, and terrible is the wreck and ruin of that house."