< Luka 6 >
1 Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
Now it happened on a second-first Sabbath that He was passing through the grain fields, and His disciples began to pick and eat the heads of grain, rubbing them in their hands.
2 Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
But some of the Pharisees said to them, “Why are you doing that which is not lawful to do on the Sabbath?”
3 Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
So in answer to them Jesus said: “Have you not even read this, what David did when he was hungry, he and those who were with him:
4 Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
how he went into the house of God, took and ate the showbread, and even gave it to those with him—that which only the priests are allowed to eat?”
5 Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
Then He said to them, “The Son of the Man is Lord even of the Sabbath!”
6 Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
Now it happened on a different Sabbath that He entered the synagogue and began to teach. Well there was a man there whose right hand was shriveled;
7 Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
so the scribes and the Pharisees started watching, to see if He would heal on the Sabbath, so that they might find an accusation against Him.
8 Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
But He knew their thoughts and said to the man with the shriveled hand, “Get up and stand in the center.” So he got up and stood.
9 Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
Then Jesus said to them: “I will ask you something: Is it lawful on the Sabbath to do good or to do evil, to save life or to kill?”
10 Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
And when He had looked around at them all, He said to him, “Stretch out your hand!” So he did that, and his hand was restored, as sound as the other.
11 Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
But they were filled with rage, and began to discuss with one another what they might do to Jesus.
12 Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
Now it happened in those days that He went out to the mountain to pray, and He continued all night in prayer to God.
13 Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
When it was day He called His disciples, and from them He chose twelve, whom He also named apostles:
14 Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
Simon (whom He also named Peter) and Andrew his brother, James and John, Phillip and Bartholomew,
15 Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
Matthew and Thomas, James (the son of Alphaeus) and Simon (the one called ‘Zealot’),
16 da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
Judas of James and Judas Iscariot (who also became ‘traitor’).
17 Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
Then He came down with them and stood on a level place, with a crowd of His disciples and a great multitude of people from all Judea and Jerusalem, also from the seacoast of Tyre and Sidon, who came to hear Him and to be healed of their diseases,
18 Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
as well as those who were being harassed by unclean spirits—and they were being healed!
19 Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
So the whole crowd kept trying to touch Him, because power was going out from Him and was healing all.
20 Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
Then He raised His eyes toward His disciples and said: “Blessed are you poor, because the Kingdom of God is yours.
21 Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
Blessed are you who hunger now, because you will be filled. Blessed are you who weep now, because you will laugh.
22 Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
Blessed are you whenever men hate you, and whenever they exclude you and heap insults on you and trash your name as ‘malignant’, for the Son of the Man's sake.
23 Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
Rejoice in that day and skip about! Because your reward really is great in Heaven; for that is how their fathers treated the prophets.
24 Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
“But woe to you who are rich! because you have already received your comfort.
25 Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
Woe to you who are full! because you will go hungry. Woe to you who are presently laughing! because you will mourn and weep.
26 Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
Woe, when all men speak well of you; for that is how their fathers treated the false prophets!
27 Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
“Further, to you who are listening I say: Love your enemies, do good to those who hate you;
28 Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
bless those who curse you, pray for those who mistreat you.
29 Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
To him who strikes you on the cheek, offer also the other; and from him who takes away your cloak, do not withhold the tunic as well.
30 Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
Give to everyone who asks of you; and from him who takes away your things, do not demand them back.
31 Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
Yes, like you want people to treat you, that is just how you must treat them.
32 Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
Also, if you love those who love you, what credit is that to you? Even ‘sinners’ love those who love them.
33 Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
And if you do good to those doing good to you, what credit is that to you? Even ‘sinners’ do the same.
34 Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
And if you lend to those from whom you expect to get it back, what credit is that to you? Even ‘sinners’ lend to ‘sinners’, to receive an equal value back.
35 Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
“So, love your enemies, and do good, and lend, expecting nothing back; and your reward will be great, and you will be sons of the Most High; because He is kind toward the ungrateful and wicked.
36 Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
So be compassionate, even as your Father is compassionate.
37 Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
“Do not judge, and you will not be judged. Do not condemn, and you will not be condemned. Forgive, and you will be forgiven.
38 Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
Give and it will be given to you: a good measure—pressed down and shaken together and running over—will they deposit in your lap. Because with the same measure that you use it will be measured back to you.”
39 Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
Then He told them a parable: “Can a blind man guide a blind man? Will they not both fall into a ditch?
40 Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
A disciple is not above his teacher, but everyone who is fully trained will be like his teacher.
41 Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
Why do you look at the speck in your brother's eye, but do not consider the plank that is in your own eye?
42 Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
Or how can you say to your brother, ‘Brother, let me remove the speck that is in your eye,’ when you yourself do not see the plank that is in your own eye? Hypocrite! First remove the plank from your own eye, and then you will see clearly to remove the speck that is in your brother's eye.
43 Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
“Now no good tree produces rotten fruit, nor does a rotten tree produce good fruit
44 Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
—each tree is known by its own fruit: people do not gather figs from thorn bushes, nor do they pick a bunch of grapes from a bramble.
45 Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
The good man produces the good out of the good treasure in his heart, and the malignant man produces the malignant out of the malignant treasure in his heart; because his mouth speaks out of the abundance of the heart.
46 Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
“Why do you call me, ‘Lord, Lord’, and not do what I say?
47 Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
Everyone who comes to me and hears my words and does them—I will show you who he is like:
48 Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
he is like a man building a house, who dug down deep and laid the foundation on the bedrock. When a flood occurred, the torrent burst upon that house but could not shake it, because it was founded on the bedrock.
49 Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
But he who heard and did nothing is like a man who built his house on the ground without a foundation, against which the torrent burst, and immediately it fell; and the ruin of that house was great.”