< Luka 6 >
1 Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
And it came to pass on [the] second-first sabbath, that he went through cornfields, and his disciples were plucking the ears and eating [them], rubbing [them] in their hands.
2 Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
But some of the Pharisees said to them, Why do ye what is not lawful to do on the sabbath?
3 Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
And Jesus answering said to them, Have ye not read so much as this, what David did when he hungered, he and those who were with him,
4 Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
how he entered into the house of God and took the shewbread and ate, and gave to those also who were with him, which it is not lawful that [any] eat, unless the priests alone?
5 Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
And he said to them, The Son of man is Lord of the sabbath also.
6 Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
And it came to pass on another sabbath also that he entered into the synagogue and taught; and there was a man there, and his right hand was withered.
7 Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
And the scribes and the Pharisees were watching if he would heal on the sabbath, that they might find something of which to accuse him.
8 Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
But he knew their thoughts, and said to the man who had the withered hand, Get up, and stand in the midst. And having risen up he stood [there].
9 Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
Jesus therefore said to them, I will ask you if it is lawful on the sabbath to do good, or to do evil? to save life, or to destroy [it]?
10 Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
And having looked around on them all, he said to him, Stretch out thy hand. And he did [so] and his hand was restored as the other.
11 Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
But they were filled with madness, and they spoke together among themselves what they should do to Jesus.
12 Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
And it came to pass in those days that he went out into the mountain to pray, and he spent the night in prayer to God.
13 Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
And when it was day he called his disciples, and having chosen out twelve from them, whom also he named apostles:
14 Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
Simon, to whom also he gave the name of Peter, and Andrew his brother, [and] James and John, [and] Philip and Bartholomew,
15 Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
[and] Matthew and Thomas, James the [son] of Alphaeus and Simon who was called Zealot,
16 da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
[and] Judas [brother] of James, and Judas Iscariote, who was also [his] betrayer;
17 Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
and having descended with them, he stood on a level place, and a crowd of his disciples, and a great multitude of the people from all Judaea and Jerusalem, and the sea coast of Tyre and Sidon, who came to hear him, and to be healed of their diseases;
18 Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
and those that were beset by unclean spirits were healed.
19 Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
And all the crowd sought to touch him, for power went out from him and healed all.
20 Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
And he, lifting up his eyes upon his disciples, said, Blessed [are] ye poor, for yours is the kingdom of God.
21 Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
Blessed ye that hunger now, for ye shall be filled. Blessed ye that weep now, for ye shall laugh.
22 Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
Blessed are ye when men shall hate you, and when they shall separate you [from them], and shall reproach [you], and cast out your name as wicked, for the Son of man's sake:
23 Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
rejoice in that day and leap for joy, for behold, your reward is great in the heaven, for after this manner did their fathers act toward the prophets.
24 Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
But woe to you rich, for ye have received your consolation.
25 Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
Woe to you that are filled, for ye shall hunger. Woe to you who laugh now, for ye shall mourn and weep.
26 Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
Woe, when all men speak well of you, for after this manner did their fathers to the false prophets.
27 Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
But to you that hear I say, Love your enemies; do good to those that hate you;
28 Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
bless those that curse you; pray for those who use you despitefully.
29 Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
To him that smites thee on the cheek, offer also the other; and from him that would take away thy garment, forbid not thy body-coat also.
30 Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
To every one that asks of thee, give; and from him that takes away what is thine, ask it not back.
31 Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
And as ye wish that men should do to you, do ye also to them in like manner.
32 Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
And if ye love those that love you, what thank is it to you? for even sinners love those that love them.
33 Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
And if ye do good to those that do good to you, what thank is it to you? for even sinners do the same.
34 Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
And if ye lend to those from whom ye hope to receive, what thank is it to you? [for] even sinners lend to sinners that they may receive the like.
35 Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
But love your enemies, and do good, and lend, hoping for nothing in return, and your reward shall be great, and ye shall be sons of [the] Highest; for he is good to the unthankful and wicked.
36 Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
Be ye therefore merciful, even as your Father also is merciful.
37 Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
And judge not, and ye shall not be judged; condemn not, and ye shall not be condemned. Remit, and it shall be remitted to you.
38 Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
Give, and it shall be given to you; good measure, pressed down, and shaken together, and running over, shall be given into your bosom: for with the same measure with which ye mete it shall be measured to you again.
39 Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
And he spoke also a parable to them: Can a blind [man] lead a blind [man]? shall not both fall into [the] ditch?
40 Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
The disciple is not above his teacher, but every one that is perfected shall be as his teacher.
41 Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
But why lookest thou on the mote which is in the eye of thy brother, but perceivest not the beam which is in thine own eye?
42 Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
or how canst thou say to thy brother, Brother, allow [me], I will cast out the mote that is in thine eye, thyself not seeing the beam that is in thine eye? Hypocrite, cast out first the beam out of thine eye, and then thou shalt see clear to cast out the mote which is in the eye of thy brother.
43 Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
For there is no good tree which produces corrupt fruit, nor a corrupt tree which produces good fruit;
44 Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
for every tree is known by its own fruit, for figs are not gathered from thorns, nor grapes vintaged from a bramble.
45 Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
The good man, out of the good treasure of his heart, brings forth good; and the wicked [man] out of the wicked, brings forth what is wicked: for out of the abundance of the heart his mouth speaks.
46 Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
And why call ye me, Lord, Lord, and do not the things that I say?
47 Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
Every one that comes to me, and hears my words and does them, I will shew you to whom he is like.
48 Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
He is like a man building a house, who dug and went deep, and laid a foundation on the rock; but a great rain coming, the stream broke upon that house, and could not shake it, for it had been founded on the rock.
49 Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
And he that has heard and not done, is like a man who has built a house on the ground without [a] foundation, on which the stream broke, and immediately it fell, and the breach of that house was great.