< Luka 5 >
1 Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
Now it happened, as he stood by the lake Gennesareth, the multitude pressing upon him to hear the word of God;
2 Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
that seeing two barks aground, near the shore, the fishermen having landed to wash their nets,
3 Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
he went aboard one of them, which was Simon's; and desiring him to put off a little from the land, sat down, and taught the people out of the bark.
4 Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
When he had done speaking, he said to Simon, Launch out into deep water, and let down your nets for a draught.
5 Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
Simon answered, Master, we have toiled all night, and have caught nothing; nevertheless, at your word, I will let down the net.
6 Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
Having done this, they inclosed such a multitude of fishes, that the net began to break.
7 Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
And they beckoned to their companions, in the other bark, to come and help them. And they came, and loaded both their barks, so that they were near sinking.
8 Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
When Simon Peter saw this, he threw himself at Jesus' knees, saying, Depart from me, Lord, for I am a sinful man.
9 Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
For the draught of fishes which they had taken had filled him and all his companions with terror,
10 Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
particularly James and John, sons of Zebedee, who were Simon's partners. And Jesus said to Simon, Fear not, henceforth you shall catch men.
11 Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
And having brought their barks to land, they forsook all, and followed him.
12 Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
When he was in one of the neighboring cities, a man covered with leprosy, happened to see him, threw himself on his face, and besought him, saying, Master, if you will, you can cleanse me.
13 Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
Jesus stretching out his hand, and touching him, said, I will; be you cleansed. That instant his leprosy departed from him.
14 Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
And he commanded him to tell no person. But go, said he, show yourself to the priest, and present the offered appointed by Moses, for notifying the people that you are cleansed.
15 Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
Yet so much the more was Jesus everywhere talked of, that vast multitudes flocked to hear him, and to be cured by him of their maladies.
16 Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
And he withdrew into solitary places, and prayed.
17 Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
One day, as he was teaching, and Pharisees, and doctors of law, who had come from Jerusalem, and from every town of Galilee and Judea, were sitting by, the power of the Lord was exerted in the sure of the sick.
18 A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
And, behold, some men carrying on a bed a man afflicted with a palsy, endeavored to bring him in, and place him before Jesus;
19 Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
but finding it impracticable, by reason of the crowd, they got upon the roof, and let him down through the tiling, with the little bed, in the midst before him.
20 Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
Jesus perceiving their faith, said, Man, your sins are forgiven you.
21 Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
On which the Scribes and the Pharisees reasoned thus, Who is this that speaks blasphemies? Can any one forgive sins except God?
22 Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
Jesus knowing their thoughts, addressed himself to them, and said, What are you reasoning in your hearts?
23 Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
Which is easier, to say, Your sins are forgiven you; or to say, Arise, and walk?
24 Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
But that you may know that the Son of Man has power on earth to forgive sins, Arise, said he to the palsied man, take up your bed, and return to your house.
25 Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
That instant he rose in their presence, took up his bed, and returned home, glorifying God.
26 Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
Seeing this, they were all struck with amazement and reverence, and glorified God, saying, We have seen wonderful things to-day.
27 Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
After this, he went out, and observing a publican, named Levi, sitting at the toll-office, said to him, Follow me.
28 Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
And he arose, left all, and followed him.
29 Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
And Levi made him a great entertainment in his own house, where there was a great company of publicans and others, at table with them.
30 Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
But the Scribes and the Pharisees of the place murmured, saying to his disciples, Why do you eat and drink with publicans and sinners?
31 Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
Jesus answering, said to them, It is not the healthy, but the sick, who need a physician.
32 Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
I am come to call, not the righteous, but sinners, to reformation.
33 Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
Then they asked him, How is it that the disciples of John, and likewise those of the Pharisees, frequently fast and pray, but yours eat and drink?
34 Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
He answered, Would you have the bridemen fast, while the bridegroom is with them?
35 Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
But the days will come, when the bridegroom shall be taken from them: in those days they will fast.
36 Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
He added this similitude, No man mends an old mantle with new cloth; otherwise the new will rend the old; besides, the old and new will never suit each other.
37 Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
No person puts new wine into old leather bottles; otherwise, the new wine will burst the bottles, and thus the wine will be spoiled, and the bottles rendered useless.
38 Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
But if new wine be put into new bottles, both will be preserved.
39 Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”
Besides, a man, after drinking old wine, calls not immediately for new; for he says, The old is milder.