< Luka 4 >

1 Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
Jeesus, täis Püha Vaimu, tuli Jordani jõe äärest tagasi ja Vaim juhtis ta kõrbesse,
2 kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
kus kurat teda nelikümmend päeva kiusas. Kogu selle aja jooksul ei söönud ta midagi, nii et lõpuks oli tal nälg.
3 Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
Kurat ütles talle: „Kui sa oled Jumala Poeg, käsi sel kivil leivaks muutuda.“
4 Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
„Pühakirjas on kirjutatud: „Inimene ei ela üksnes leivast, ““vastas Jeesus.
5 Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
Kurat viis ta üles kõrgesse kohta ja näitas talle põgusalt kõiki maailma kuningriike.
6 Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
Seejärel ütles kurat Jeesusele: „Ma annan sulle võimu kõigi nende üle ja nende hiilguse. See võim on antud mulle ja mina võin anda selle, kellele tahan.
7 Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
Kummarda maani ja teeni mind ning sa võid kõik selle saada.“
8 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
„Pühakirjas on kirjutatud: „Sina pead kummardama Issandat, oma Jumalat, ja üksnes teda teenima, ““vastas Jeesus.
9 Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
Kurat viis Jeesuse Jeruusalemma, asetas ta templi katusele ja ütles talle: „Kui sa oled Jumala Poeg, siis hüppa!
10 Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
Sest Pühakirjas on kirjutatud: „Ta käsib oma inglitel sinu eest hoolitseda
11 kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
ja sind kaitsta, et sa kivi otsa ei komistaks“.“
12 Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
„Pühakirjas on kirjutatud: „Sa ei tohi Issandat, oma Jumalat, kiusata, ““vastas Jeesus.
13 Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
Kui kurat oli kõik oma kiusatused lõpetanud, jäi ta järgmist võimalust ootama.
14 Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
Jeesus läks Vaimu väega täidetult Galileasse tagasi. Kuuldused temast levisid kõikjal.
15 Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
Jeesus õpetas nende sünagoogides ja kõik ülistasid teda.
16 Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
Kui ta jõudis Naatsaretti, kus ta oli üles kasvanud, läks ta hingamispäeval sünagoogi nagu tavaliselt.
17 An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
Talle ulatati prohvet Jesaja rullraamat. Jeesus keeras kirjarulli lahti ja leidis koha, kus on kirjutatud:
18 “Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
„Issanda Vaim on minu peal, sest ta on mind võidnud kuulutama head sõnumit vaestele. Ta on saatnud mind teatama, et vangid vabastatakse, pimedad näevad, rõhutud vabanevad,
19 in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
kuulutama välja Issandale meelepärast aega.“
20 Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
Ta keeras pärgamendirulli kokku ja andis teenrile tagasi. Siis istus ta maha. Kõik sünagoogis vaatasid tema poole.
21 Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
„See Pühakirja tekst, mida te just kuulsite, on täna täide läinud!“ütles ta neile.
22 Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
Kõik väljendasid oma heakskiitu ja olid hämmastunud neist meeldivatest sõnadest, mis tema huulilt tulid. „Kas see pole Joosepi poeg?“imestasid nad.
23 Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
Jeesus vastas: „Olen kindel, et kordate mulle seda vanasõna: „Arst, ravi ennast!“, ja küsite: „Miks ei tee sa siin, oma kodulinnas, seda, mida sa kuuldavasti Kapernaumas tegid?“
24 Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
Aga ma ütlen teile tõtt, ühtki prohvetit ei tunnustata tema kodulinnas.
25 Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
Olen kindel, et Eelija ajal oli Iisraelis palju lesknaisi, kui kolm ja pool aastat oli põud, mis põhjustas riigis suure näljahäda.
26 Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
Ometi ei saadetud Eelijat ühegi juurde neist. Ta saadeti lesknaise juurde Sareptas, Siidoni piirkonnas!
27 Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
Kuigi Eliisa ajal oli Iisraelis palju pidalitõbiseid, oli ainus, kes terveks sai, süürlane Naaman!“
28 Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
Kui sünagoogis viibijad seda kuulsid, said nad kõik maruvihaseks.
29 Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
Nad hüppasid püsti ja viskasid ta linnast välja. Siis vedasid nad ta künka otsa, mille peale linn oli ehitatud, et teda kaljult alla visata.
30 Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
Aga tema kõndis otse nende vahelt läbi ja läks oma teed.
31 Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
Jeesus läks alla Kapernauma, ühte Galilea linna. Hingamispäeval hakkas ta neid õpetama.
32 Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
Nad olid hämmastunud sellest, mida ta neile õpetas, sest ta kõneles mõjuvõimsalt.
33 A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
Sünagoogis oli üks mees, kes oli kurja vaimu valduses. Ta hüüdis:
34 “Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
„Mida sa meist tahad, Naatsareti Jeesus? Kas sa tulid meid hävitama? Ma tean, kes sa oled: Jumala Püha!“
35 Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
Jeesus katkestas teda ja ütles: „Ole vait!“Seejärel käskis ta kurja vaimu: „Tule temast välja!“Kuri vaim heitis mehe nende ette maha ja lahkus temast, ilma teda vigastamata.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
Nad kõik olid hämmastuses ja küsisid üksteiselt: „Mis õpetus see on? Ta käsib väe ja võimuga kurjadel vaimudel lahkuda ja nad teevad seda!“
37 Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
Kuuldused Jeesusest levisid kogu ümbruskonnas.
38 Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
Sünagoogist lahkudes läks Jeesus Siimona koju. Siimona ämm oli kõrges palavikus haige ja need, kes seal viibisid, palusid Jeesuselt abi.
39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
Jeesus läks ja seisis tema juurde. Ta käskis palavikul naisest lahkuda ja nii sündis. Naine tõusis kohe püsti ja valmistas neile süüa.
40 Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
Kui päike loojus, tõid nad tema juurde kõik, kes olid haiged, kes kannatasid mitmesuguste vaevuste all. Jeesus pani oma käed üksteise järel nende peale ja tegi nad terveks.
41 Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
Paljudest inimestest tulid kurjad vaimud välja ja karjusid: „Sa oled Jumala Poeg!“Aga Jeesus takistas neid ega lasknud neil rääkida, sest nad teadsid, et ta on Kristus.
42 Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
Jeesus lahkus järgmisel hommikul vara, et leida mõni rahulik ja vaikne koht. Kuid rahvahulk läks välja teda otsima ja lõpuks ka leidis. Nad üritasid tema lahkumist takistada, sest nad ei tahtnud, et ta ära läheks.
43 Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
Kuid tema ütles neile: „Ma pean minema teistesse linnadesse, et rääkida ka neile head sõnumit Jumala riigist, sest selleks on mind läkitatud.“
44 Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
Nii rändas Jeesus ringi ja õpetas Juudamaa sünagoogides head sõnumit.

< Luka 4 >