< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being Governor of Judaea, Herod Tetrarch of Galilee, his brother Philip Tetrarch of Ituraea and Trachonitis, and Lysanias Tetrarch of Abilene,
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
during the High-priesthood of Annas and Caiaphas, a message from God came to John, the son of Zechariah, in the Desert.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
John went into all the district about the Jordan proclaiming a baptism of the penitent for the forgiveness of sins;
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
as it is written in the book of the prophet Isaiah, "The voice of one crying aloud! 'In the Desert prepare ye a road for the Lord: make His highway straight.
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
Every ravine shall be filled up, and every mountain and hill levelled down, the crooked places shall be turned into straight roads, and the rugged ways into smooth;
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
and then shall all mankind see God's salvation.'"
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Accordingly John used to say to the crowds who came out to be baptized by him, "O vipers' brood, who has warned you to flee from the coming wrath?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Live lives which shall prove your change of heart; and do not begin to say to yourselves, 'We have Abraham as our forefather,' for I tell you that God can raise up descendants for Abraham from these stones.
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
And even now the axe is lying at the root of the trees, so that every tree which fails to yield good fruit will quickly be hewn down and thrown into the fire."
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
The crowds repeatedly asked him, "What then are we to do?"
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
"Let the man who has two coats," he answered, "give one to the man who has none; and let the man who has food share it with others."
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
There came also a party of tax-gatherers to be baptized, and they asked him, "Rabbi, what are we to do?"
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
"Do not exact more than the legal amount," he replied.
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
The soldiers also once and again inquired of him, "And we, what are we to do?" His answer was, "Neither intimidate any one nor lay false charges; and be content with your pay."
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
And while the people were in suspense and all were debating in their minds whether John might possibly be the Anointed One,
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
he answered the question by saying to them all, "As for me, I am baptizing you with water, but One mightier than I is coming, whose very sandal-strap I am not worthy to unfasten: He will baptize you in the Holy Spirit and with fire.
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
His winnowing-shovel is in His hand to clear out His threshing-floor, and to gather the wheat into His storehouse; but the chaff He will burn up in fire unquenchable."
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
With many exhortations besides these he declared the Good News to the people.
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
But Herod the Tetrarch, being repeatedly rebuked by him about Herodias his brother's wife, and about all the wicked deeds that he had done,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
now added this to crown all the rest, that he threw John into prison.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Now when all the people had been baptized, and Jesus also had been baptized and was praying, the sky opened,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
and the Holy Spirit came down in bodily shape, like a dove, upon Him, and a voice came from Heaven, which said, "Thou art My Son, dearly loved: in Thee is My delight."
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
And He--Jesus--when He began His ministry, was about thirty years old. He was the son (it was supposed) of Joseph, son of Heli,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
son of Matthat, son of Levi, son of Melchi, son of Jannai, son of Joseph,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
son of Mattathias, son of Amos, son of Nahum, son of Esli, son of Naggai,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
son of Mahath, son of Mattathias, son of Semein, son of Josech, son of Joda,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
son of Johanan, son of Resa, son of Zerubbabel, son of Shealtiel, son of Neri,
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
son of Melchi, son of Addi, son of Cosam, son of Elmadam, son of Er,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
son of Joshua, son of Eliezar, son of Jorim, son of Maththat, son of Levi,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
son of Symeon, son of Judah, son of Joseph, son of Jonam, son of Eliakim, son of
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
Melea, son of Menna, son of Mattatha, son of Nathan, son of David,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
son of Jesse, son of Obed, son of Boaz, son of Salmon, son of Nahshon,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
son of Amminadab, son of Admin, son of Arni, son of Hezron, son of Perez, son of Judah,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
son of Jacob, son of Isaac, son of Abraham, son of Terah, son of Nahor,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
son of Serug, son of Reu, son of Peleg, son of Eber, son of Shelah,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
son of Cainan, son of Arpachshad, son of Shem, son of Noah, son of Lamech,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
son of Methuselah, son of Enoch, son of Jared, son of Mahalalel, son of Kenan,
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
son of Enosh, son of Seth, son of Adam, son of God.

< Luka 3 >