< Luka 24 >
1 Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
And on the first day of the week, at early dawn, they came to the sepulcher, bringing the spices which they had prepared; and with them came certain others.
2 Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
And they found the stone rolled away from the sepulcher;
3 Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
and they entered in, but found not the body of the Lord Jesus.
4 Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
And it came to pass, while they were much perplexed at this, behold, two men stood by them in shining raiment.
5 Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
And while they feared and bowed their faces to the earth, they said to them: Why seek you among the dead for him that lives?
6 Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
He is not here, but he has risen; remember that he spoke to you while he was yet in Galilee,
7 cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
saying, The Son of man must be delivered into the hands of sinful men, and be crucified, and the third day rise again.
8 Sai matan suka tuna da kalmominsa,
And they remembered his words,
9 suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
and returned from the sepulcher, and told all these things to the eleven and to the rest.
10 Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
It was Mary Magdalene and Joanna and Mary the mother of James, and the others with them, that told these things to the apostles.
11 Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
And their words seemed to them as idle tales, and they believed them not.
12 Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
But Peter arose and ran to the sepulcher, and stooping down, he saw the linen clothes lying by themselves; and he departed, wondering in himself at that which had come to pass.
13 A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
And, behold, two of them were going, on the same day, to a village called Emmaus, distant from Jerusalem sixty furlongs.
14 Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
And they were talking to one another about all these things which had taken place.
15 Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
And it came to pass, that, while they conversed and reasoned together, Jesus himself drew near, and went on with them.
16 Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
But their eyes were restrained, so that they did not recognize him.
17 Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
And he said to them: What matters are these which you are discussing with one another as you walk and are sad?
18 Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
And one of them, whose name was Cleopas, answered and said to him: Are you only a stranger in Jerusalem, and have not known the things that have taken place there in these days?
19 Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
And he said to them: What things? They said to him: The things concerning Jesus the Nazarene, who was a prophet mighty in deed and in word before God and all the people;
20 Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
and how the chief priests and our rulers delivered him up to be condemned to death, and crucified him.
21 Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
But we trusted that it was he that was about to redeem Israel. And besides all this, to-day is the third day since these things were done.
22 Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
And further, certain women of our company, who were early at the sepulcher, astonished us:
23 Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
for they found not his body, and came and told that they had seen a vision of angels, who said that he was alive.
24 Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
And some of those who were with us went to the sepulcher, and found it even as the women had said, but him they saw not.
25 Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
And he said to them: O inconsiderate, and slow of heart to believe all things that the prophets have spoken!
26 Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
Ought not the Christ to have suffered these things, and to enter into his glory?
27 Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
And beginning from Moses, and all the prophets, he explained to them, in all the Scriptures, the things concerning himself.
28 Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
And they drew near the village to which they were going; and he made as if he would go further.
29 Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
And they constrained him, saying: Remain with us, for it is near the evening, and the day has declined. And he went in to remain with them.
30 Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
And it came to pass, while he reclined at table with them, that he took bread and blessed; and he broke, and gave it to them.
31 Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
And their eyes were opened, and they recognized him, and he disappeared from them.
32 Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
And they said one to another, Did not our heart burn within us while he talked with us by the way, and while he opened to us the scriptures?
33 Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
And they arose the same hour, and returned to Jerusalem, and found the eleven, and those who were with them, assembled,
34 cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
and saying: The Lord has risen indeed, and has appeared to Simon.
35 Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
And they told what had taken place on the way, and how he was made known to them in the breaking of bread.
36 Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
And while they were speaking of these things, Jesus him self stood in the midst of them, and said to them: Peace be to you.
37 Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
But they were terrified and frightened, and thought that they saw a spirit.
38 Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
And he said to them: Why are you troubled, and why do doubts arise in your hearts?
39 Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
See my hands and my feet, that it is I myself; handle me and see; for a spirit has not flesh and bones, as you see me have.
40 Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
And when he had said this, he showed them his hands and his feet.
41 Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
And while they did not believe as yet for joy, and were astonished, he said to them: Have you any thing here to eat?
42 Sai suka bashi gasasshen kifi.
And they gave him a piece of broiled fish, and of a honeycomb.
43 Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
And he took it, and did eat before them.
44 Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
And he said to them: These are the words that I spoke to you, while I was yet with you, that all things must be fulfilled that are written in the law of Moses, and in the prophets, and in the psalms, concerning me.
45 Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
Then he opened their mind, that they might understand the scriptures,
46 Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
and he said to them: Thus it is written, and thus was it necessary that the Christ should suffer, and rise again from the dead the third day,
47 Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
and that repentance and remission of sins should be preached in his name among all nations, beginning at Jerusalem.
48 Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
You are witnesses of these things.
49 Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
And behold, I send the promise of my Father upon you. But do you remain in the city of Jerusalem, till you be clothed with power from on high.
50 Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
And he led them out as far as Bethany; and he lifted up his hands and blessed them.
51 Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
And it came to pass, that as he blessed them, he was separated from them, and carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
And they worshiped him, and returned to Jerusalem with great joy;
53 Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.
and were continually in the temple, praising and blessing God.