< Luka 23 >
1 Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
And the whole multitude of them rising up, led him to Pilate.
2 Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
And they began to accuse him, saying: We have found this man perverting our nation, and forbidding to give tribute to Caesar, and saying that he is Christ the king.
3 Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
And Pilate asked him, saying: Art thou the king of the Jews? But he answering, said: Thou sayest it.
4 Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
And Pilate said to the chief priests and to the multitudes: I find no cause in this man.
5 Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
But they were more earnest, saying: He stirreth up the people, teaching throughout all Judea, beginning from Galilee to this place.
6 Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
But Pilate hearing Galilee, asked if the man were of Galilee?
7 Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
And when he understood that he was of Herod’s jurisdiction, he sent him away to Herod, who was also himself at Jerusalem, in those days.
8 Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
And Herod, seeing Jesus, was very glad; for he was desirous of a long time to see him, because he had heard many things of him; and he hoped to see some sign wrought by him.
9 Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
And he questioned him in many words. But he answered him nothing.
10 Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
And the chief priests and the scribes stood by, earnestly accusing him.
11 Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
And Herod with his army set him at nought, and mocked him, putting on him a white garment, and sent him back to Pilate.
12 Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
And Herod and Pilate were made friends, that same day; for before they were enemies one to another.
13 Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
And Pilate, calling together the chief priests, and the magistrates, and the people,
14 sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
Said to them: You have presented unto me this man, as one that perverteth the people; and behold I, having examined him before you, find no cause in this man, in those things wherein you accuse him.
15 Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
No, nor Herod neither. For I sent you to him, and behold, nothing worthy of death is done to him.
16 saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
I will chastise him therefore, and release him.
17 [Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
Now of necessity he was to release unto them one upon the feast day.
18 Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
But the whole multitude together cried out, saying: Away with this man, and release unto us Barabbas:
19 Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
Who, for a certain sedition made in the city, and for a murder, was cast into prison.
20 Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
And Pilate again spoke to them, desiring to release Jesus.
21 Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
But they cried again, saying: Crucify him, crucify him.
22 Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
And he said to them the third time: Why, what evil hath this man done? I find no cause of death in him. I will chastise him therefore, and let him go.
23 Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
But they were instant with loud voices, requiring that he might be crucified; and their voices prevailed.
24 Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
And Pilate gave sentence that it should be as they required.
25 Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
And he released unto them him who for murder and sedition, had been cast into prison, whom they had desired; but Jesus he delivered up to their will.
26 Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
And as they led him away, they laid hold of one Simon of Cyrene, coming from the country; and they laid the cross on him to carry after Jesus.
27 Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
And there followed him a great multitude of people, and of women, who bewailed and lamented him.
28 Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
But Jesus turning to them, said: Daughters of Jerusalem, weep not over me; but weep for yourselves, and for your children.
29 Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
For behold, the days shall come, wherein they will say: Blessed are the barren, and the wombs that have not borne, and the paps that have not given suck.
30 Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
Then shall they begin to say to the mountains: Fall upon us; and to the hills: Cover us.
31 Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
For if in the green wood they do these things, what shall be done in the dry?
32 Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
And there were also two other malefactors led with him to be put to death.
33 Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
And when they were come to the place which is called Calvary, they crucified him there; and the robbers, one on the right hand, and the other on the left.
34 Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
And Jesus said: Father, forgive them, for they know not what they do. But they, dividing his garments, cast lots.
35 Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
And the people stood beholding, and the rulers with them derided him, saying: He saved others; let him save himself, if he be Christ, the elect of God.
36 Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
And the soldiers also mocked him, coming to him, and offering him vinegar,
37 suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
And saying: If thou be the king of the Jews, save thyself.
38 Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
And there was also a superscription written over him in letters of Greek, and Latin, and Hebrew: THIS IS THE KING OF THE JEWS.
39 Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
And one of those robbers who were hanged, blasphemed him, saying: If thou be Christ, save thyself and us.
40 Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
But the other answering, rebuked him, saying: Neither dost thou fear God, seeing thou art condemned under the same condemnation?
41 Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
And we indeed justly, for we receive the due reward of our deeds; but this man hath done no evil.
42 Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
And he said to Jesus: Lord, remember me when thou shalt come into thy kingdom.
43 Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
And Jesus said to him: Amen I say to thee, this day thou shalt be with me in paradise.
44 Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
And it was almost the sixth hour; and there was darkness over all the earth until the ninth hour.
45 sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
And the sun was darkened, and the veil of the temple was rent in the midst.
46 Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
And Jesus crying out with a loud voice, said: Father, into thy hands I commend my spirit. And saying this, he gave up the ghost.
47 Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
Now the centurion, seeing what was done, glorified God, saying: Indeed this was a just man.
48 Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
And all the multitude of them that were come together to that sight, and saw the things that were done, returned striking their breasts.
49 Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
And all his acquaintance, and the women that had followed him from Galilee, stood afar off, beholding these things.
50 Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
And behold there was a man named Joseph, who was a counsellor, a good and just man,
51 (bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
(The same had not consented to their counsel and doings; ) of Arimathea, a city of Judea; who also himself looked for the kingdom of God.
52 Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
This man went to Pilate, and begged the body of Jesus.
53 Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
And taking him down, he wrapped him in fine linen, and laid him in a sepulchre that was hewed in stone, wherein never yet any man had been laid.
54 Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
And it was the day of the Parasceve, and the sabbath drew on.
55 Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
And the women that were come with him from Galilee, following after, saw the sepulchre, and how his body was laid.
56 Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.
And returning, they prepared spices and ointments; and on the sabbath day they rested, according to the commandment.