< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Ringi vaadates jälgis Jeesus, kuidas jõukad inimesed panid oma annetusi kogumiskasti.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Ta nägi ka, kuidas üks väga vaene lesknaine pani sinna kaks pisikest münti.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
„Ma räägin teile tõtt, “ütles ta, „see vaene lesknaine pani kasti rohkem kui kõik ülejäänud kokku.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
Kõik nad andsid oma jõukusest, mis neil oli, kuid tema andis oma vaesusest kõik, millest ta pidi elama.“
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Mõned neist seal rääkisid templist, selle peenelt tahutud kividest ja suurepärastest annetustest, mida nad andnud olid. Aga Jeesus ütles:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
„Nende asjade kohta, mida te silmas peate: tuleb aeg, mil ei jäeta üht kivi teise peale, kõik hävitatakse!“
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
„Õpetaja, millal see toimub?“küsisid nad talt. „Missugune on märk, et need asjad hakkavad toimuma?“
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
„Veenduge, et teid ei petetaks, “hoiatas Jeesus neid. „Paljud tulevad ja väidavad, et nad on mina, öeldes: „Siin ma olen!“ja „Aeg on käes!“, aga ärge neid järgige.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Kui te kuulete sõdadest ja revolutsioonidest, ärge ehmuge, sest kõigepealt peavad need asjad toimuma, kuid lõpp ei tule kohe.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Rahvas sõdib rahvaga ja kuningriik kuningriigiga, “ütles ta neile.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
„Paljudes maades on ränki maavärinaid, näljahädasid ja haiguste epideemiaid ning erakordseid märke taevas, mis kohutavad.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Aga enne kõike seda võtavad nad teid kinni ja kiusavad taga. Nad veavad teid sünagoogide ette ja heidavad vanglasse, nad viivad teid minu pärast kohtusse kuningate ja maavalitsejate ette.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Aga see annab teile võimaluse kõneleda nende ees minust.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Niisiis, otsustage juba ette, et te ei muretse sellepärast, kuidas end kaitsta,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
sest mina annan teile tarkusesõnad, mida teie vaenlased ei suuda vaidlustada ega ümber lükata.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Teid reedavad isegi teie vanemad, vennad ja sõbrad ning nad tapavad teist mõned.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Kõik vihkavad teid minu pärast.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Aga teie peast ei lähe kaotsi ainsatki juuksekarva.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Kindlalt seistes võidate oma elu.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Aga kui te näete, et sõjaväed piiravad Jeruusalemma ümber, siis teate, et selle hävitus on lähedal.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Kes on Juudamaal, peaksid põgenema mägedesse, ja kes on Jeruusalemmas, peaksid lahkuma, ning need, kes on maal, ei tohiks linna minna.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Sest need on karistuse päevad, mis täidavad kõik, mida on kirjutatud.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Kui raske on neil, kes on sel ajal lapseootel või imetavad! Sest kohutav kitsikus on tulemas maa peale ja karistus selle elanikele.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Kõik rahvad tapavad neid mõõgaga ja viivad neid vangi. Võõrad rahvad tallavad Jeruusalemma maha, kuni nende aeg täis saab.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Päikeses, kuus ja tähtedes on märke ning rahvad maa peal on ahastuses ja segaduses mere lainetuse ja pealetungimise tõttu.
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Inimesed on hirmust nõrgad ning kohkunud sellest, mis maailmas toimub, sest taeva vägesid kõigutatakse.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Siis näevad nad inimese Poega tulemas pilves väe ja suure hiilgusega.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Aga kui see kõik juhtub, siis tõuske ja vaadake üles, sest varsti olete te päästetud.“
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Siis jutustas ta neile näitlikustamiseks selle loo. „Vaadake viigipuud või mõnda muud puud.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Kui te näete uusi lehti ilmumas, siis pole vaja teile öelda, et suvi on lähedal.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Samamoodi siis, kui te näete neid asju toimumas, ei ole teile vaja öelda, et Jumala riik on lähedal.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Ma räägin teile tõtt: see põlvkond ei lõpe enne, kui see kõik toimub.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Taevas ja maa kaovad, aga minu sõnad ei kao.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Olge ettevaatlikud, et pidutsemine või purjutamine või selle elu mured teie tähelepanu kõrvale ei juhiks, nii et see päev tabaks teid üllatusena.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Sest see päev tabab kõiki, kes elavad maa peal.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Olge alati valvel ja palvetage, et te oleksite võimelised pääsema kõigest, mis toimub, ja seisma inimese Poja ees.“
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Iga päev õpetas Jeesus templis ja igal õhtul läks ta ning jäi Õlimäele.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Kogu rahvas tuli hommikul vara teda templisse kuulama.

< Luka 21 >