< Luka 20 >
1 Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
Un de ces jours-là, comme il instruisait le peuple dans le Temple et lui annonçait l'Évangile, survinrent les chefs des prêtres et les Scribes, réunis aux Anciens,
2 Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
qui lui tinrent ce langage: «Dis-nous en vertu de quelle autorité tu fais ces choses, ou qui est celui qui t'a donné cette autorité?»
3 Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
Il leur fit cette réponse: «Je vous poserai, moi aussi, une question: répondez-moi;
4 da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
le baptême de Jean venait-il du ciel ou des hommes?»
5 Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
Or ils faisaient, à part eux, ce raisonnement: «Si nous disons: du ciel, il répliquera: «Pourquoi alors ne l'avez-vous pas cru?»
6 Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
Si nous disons: des hommes, tout le peuple nous lapidera; car il est convaincu que Jean était un prophète.»
7 Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
Ils répondirent donc qu'ils ne savaient d'où venait ce baptême.
8 Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
Et Jésus leur répondit à son tour: «Je ne vous dis pas, moi non plus, en vertu de quelle autorité je fais ces choses.»
9 Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
Puis il se mit à raconter au peuple cette parabole: «Un homme planta une vigne, la loua à des vignerons et fit une longue absence.
10 Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
La saison venue, il envoya un serviteur aux vignerons, chargé de recevoir le produit de la vigne. Les vignerons, après l'avoir battu, le renvoyèrent les mains vides.
11 Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
Le maître alors leur envoya un autre serviteur. Celui-là, ils le battirent aussi, le traitèrent avec mépris et le renvoyèrent les mains vides.
12 Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
Il leur en envoya un troisième. Celui-là ils le couvrirent de blessures et le jetèrent dehors.
13 Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
— «Que dois-je faire?» dit alors le maître de la vigne. «Je leur enverrai mon fils, mon bien-aimé; sans doute, ils le respecteront.»
14 Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
Mais quand les vignerons le virent, ils firent entre eux ce raisonnement: Celui-là c'est l'héritier; tuons-le pour que l'héritage soit à nous.»
15 Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
Alors ils le jetèrent hors de la vigne et le tuèrent. Que leur fera donc le maître de la vigne?
16 Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
Il viendra, il fera périr ces vignerons et donnera la vigne, à d'autres.» — «Que cela n'arrive pas!» dirent-ils à ces paroles.
17 Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
Mais lui, les regardant en face, ajouta: «Qu'est-ce donc que ce passage de l'Écriture: «La pierre qu'ont rejetée ceux qui bâtissaient; Celle-là même est devenue la tête de l'angle.»
18 Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
«Quiconque tombera sur cette pierre s'y brisera; et celui sur qui elle tombera, elle le mettra en poussière.»
19 Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
Les Scribes et les chefs des prêtres cherchèrent à mettre immédiatement la main sur lui; car ils comprenaient bien que c'était eux qu'il avait en vue dans cette parabole; mais ils redoutaient le peuple.
20 Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
Ils le surveillèrent et lui envoyèrent d'habiles espions qui faisaient semblant d'être de bonne foi; leur but était de surprendre une parole de lui qui leur permît de le livrer aux autorités et au pouvoir du procurateur.
21 Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
Ils lui posèrent une question: «Maître, nous savons que tu es droit dans ta parole et dans ton enseignement, que tu ne fais acception de personne, que, tout au contraire, tu enseignes en toute vérité la voie de Dieu.
22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
Nous est-il permis, oui ou non, de payer un tribut à César?»
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
Devinant leur ruse, Jésus leur dit:
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
«Montrez-moi un denier... De qui porte-t-il l'image et l'inscription?» — «De César», répondirent-ils. —
25 Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
«Eh bien, leur dit-il alors, rendez à César ce qui est à César et à Dieu ce qui est à Dieu.»
26 Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
Il leur fut ainsi impossible de surprendre une parole de lui en présence du peuple, et tout étonnés de cette réponse, ils gardèrent le silence.
27 Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
Survinrent ensuite quelques Saducéens (ceux qui affirment qu’il n’y a point de résurrection); ils lui posèrent aussi une question:
28 suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
«Maître, dirent-ils, voici ce que Moïse nous a prescrit: «Si le frère de quelqu'un meurt laissant une femme sans enfants, celui-ci devra épouser la veuve, pour susciter à son frère une postérité.»
29 Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
Or, il y a eu sept frères. Le premier a pris femme et est mort sans enfants.
Le second a épousé la veuve;
31 Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
puis le troisième; tous les sept; aucun n'a laissé d'enfants; et tous sont morts.
32 Daga baya sai matar ma ta mutu.
Enfin, la femme aussi est morte.
33 To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
Eh bien, à la résurrection, duquel d'entre eux cette femme sera-t-elle l'épouse? Les sept, en effet, l'ont eue pour femme.»
34 Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn )
Jésus leur répondit: «Les enfants de ce monde se marient et donnent en mariage; (aiōn )
35 Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn )
mais ceux qui ont été jugés dignes de participer au monde à venir et à la résurrection d'entre les morts, ne se marient, ni ne sont donnés en mariage; (aiōn )
36 Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
car ils ne peuvent plus mourir: ils sont semblables aux anges, et ils sont fils de Dieu étant fils de la résurrection.
37 Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
Or que les morts ressuscitent, Moïse l'a montré au passage du buisson, quand il appelle le Seigneur, le Dieu d'Abraham, le Dieu d'Isaac, le Dieu de Jacob.
38 Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
Or ce n'est point de morts, c'est de vivants qu'il est Dieu. Pour lui ils vivent tous.»
39 Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
Quelques Scribes intervinrent pour dire: «Maître, tu as parfaitement répondu.»
40 Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
Personne n'osait plus lui poser une seule question.
41 Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
Il leur demanda alors: «Comment dit-on que le Christ est Fils de David,
42 Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
quand David dit lui-même au livre des Psaumes: «Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Siège à ma droite;
43 sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
Jusqu'à ce que j'aie mis tes ennemis sous tes pieds.»
44 Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
Ainsi David l'appelle Seigneur, comment donc est-il son fils?»
45 Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
Devant tout le peuple qui entendait, il dit aux disciples:
46 “Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
«Soyez sur vos gardes avec les Scribes qui se complaisent à se promener en robes solennelles, qui aiment à recevoir des salutations sur les places publiques, à occuper les premiers sièges dans les synagogues, les premières places dans les festins,
47 Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”
qui dévorent, les ressources des veuves, et qui affectent de prier longuement. C'est pour ces hommes-là que le jugement aura le plus de rigueur.»