< Luka 2 >
1 Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
factum est autem in diebus illis exiit edictum a Caesare Augusto ut describeretur universus orbis
2 Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
haec descriptio prima facta est praeside Syriae Cyrino
3 Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
et ibant omnes ut profiterentur singuli in suam civitatem
4 Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
ascendit autem et Ioseph a Galilaea de civitate Nazareth in Iudaeam civitatem David quae vocatur Bethleem eo quod esset de domo et familia David
5 Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
ut profiteretur cum Maria desponsata sibi uxore praegnate
6 Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
factum est autem cum essent ibi impleti sunt dies ut pareret
7 Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
et peperit filium suum primogenitum et pannis eum involvit et reclinavit eum in praesepio quia non erat eis locus in diversorio
8 A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
et pastores erant in regione eadem vigilantes et custodientes vigilias noctis supra gregem suum
9 Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
et ecce angelus Domini stetit iuxta illos et claritas Dei circumfulsit illos et timuerunt timore magno
10 Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
et dixit illis angelus nolite timere ecce enim evangelizo vobis gaudium magnum quod erit omni populo
11 Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
quia natus est vobis hodie salvator qui est Christus Dominus in civitate David
12 Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
et hoc vobis signum invenietis infantem pannis involutum et positum in praesepio
13 Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
et subito facta est cum angelo multitudo militiae caelestis laudantium Deum et dicentium
14 “Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
gloria in altissimis Deo et in terra pax in hominibus bonae voluntatis
15 Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
et factum est ut discesserunt ab eis angeli in caelum pastores loquebantur ad invicem transeamus usque Bethleem et videamus hoc verbum quod factum est quod fecit Dominus et ostendit nobis
16 Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
et venerunt festinantes et invenerunt Mariam et Ioseph et infantem positum in praesepio
17 Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
videntes autem cognoverunt de verbo quod dictum erat illis de puero hoc
18 Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
et omnes qui audierunt mirati sunt et de his quae dicta erant a pastoribus ad ipsos
19 Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
Maria autem conservabat omnia verba haec conferens in corde suo
20 Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
et reversi sunt pastores glorificantes et laudantes Deum in omnibus quae audierant et viderant sicut dictum est ad illos
21 Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
et postquam consummati sunt dies octo ut circumcideretur vocatum est nomen eius Iesus quod vocatum est ab angelo priusquam in utero conciperetur
22 Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
et postquam impleti sunt dies purgationis eius secundum legem Mosi tulerunt illum in Hierusalem ut sisterent eum Domino
23 Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
sicut scriptum est in lege Domini quia omne masculinum adaperiens vulvam sanctum Domino vocabitur
24 Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
et ut darent hostiam secundum quod dictum est in lege Domini par turturum aut duos pullos columbarum
25 Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
et ecce homo erat in Hierusalem cui nomen Symeon et homo iste iustus et timoratus expectans consolationem Israhel et Spiritus Sanctus erat in eo
26 An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
et responsum acceperat ab Spiritu Sancto non visurum se mortem nisi prius videret Christum Domini
27 Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
et venit in Spiritu in templum et cum inducerent puerum Iesum parentes eius ut facerent secundum consuetudinem legis pro eo
28 sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
et ipse accepit eum in ulnas suas et benedixit Deum et dixit
29 “Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
nunc dimittis servum tuum Domine secundum verbum tuum in pace
30 Domin idanuna sun ga cetonka,
quia viderunt oculi mei salutare tuum
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
quod parasti ante faciem omnium populorum
32 Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
lumen ad revelationem gentium et gloriam plebis tuae Israhel
33 Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
et erat pater eius et mater mirantes super his quae dicebantur de illo
34 Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
et benedixit illis Symeon et dixit ad Mariam matrem eius ecce positus est hic in ruinam et resurrectionem multorum in Israhel et in signum cui contradicetur
35 Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
et tuam ipsius animam pertransiet gladius ut revelentur ex multis cordibus cogitationes
36 Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
et erat Anna prophetissa filia Phanuhel de tribu Aser haec processerat in diebus multis et vixerat cum viro suo annis septem a virginitate sua
37 sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
et haec vidua usque ad annos octoginta quattuor quae non discedebat de templo ieiuniis et obsecrationibus serviens nocte ac die
38 A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
et haec ipsa hora superveniens confitebatur Domino et loquebatur de illo omnibus qui expectabant redemptionem Hierusalem
39 Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
et ut perfecerunt omnia secundum legem Domini reversi sunt in Galilaeam in civitatem suam Nazareth
40 Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
puer autem crescebat et confortabatur plenus sapientia et gratia Dei erat in illo
41 Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
et ibant parentes eius per omnes annos in Hierusalem in die sollemni paschae
42 Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
et cum factus esset annorum duodecim ascendentibus illis in Hierosolymam secundum consuetudinem diei festi
43 Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
consummatisque diebus cum redirent remansit puer Iesus in Hierusalem et non cognoverunt parentes eius
44 Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
existimantes autem illum esse in comitatu venerunt iter diei et requirebant eum inter cognatos et notos
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
et non invenientes regressi sunt in Hierusalem requirentes eum
46 Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
et factum est post triduum invenerunt illum in templo sedentem in medio doctorum audientem illos et interrogantem
47 Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
stupebant autem omnes qui eum audiebant super prudentia et responsis eius
48 Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
et videntes admirati sunt et dixit mater eius ad illum fili quid fecisti nobis sic ecce pater tuus et ego dolentes quaerebamus te
49 Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
et ait ad illos quid est quod me quaerebatis nesciebatis quia in his quae Patris mei sunt oportet me esse
50 Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
et ipsi non intellexerunt verbum quod locutus est ad illos
51 Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
et descendit cum eis et venit Nazareth et erat subditus illis et mater eius conservabat omnia verba haec in corde suo
52 Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.
et Iesus proficiebat sapientia aetate et gratia apud Deum et homines