< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
Jesus and his disciples entered Jericho and were going through the [city].
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
There was a man [there] named Zacchaeus. He was a chief tax collector, who was rich.
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
He tried to see Jesus, but he was very short, and there was a big crowd of people [near Jesus]. So he was not able to see him.
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
So he ran further ahead [along the road] that Jesus was walking on. He climbed a sycamore-fig tree to see Jesus.
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
When Jesus got there, he looked up and said to him, “Zacchaeus, come down quickly, because [God wants] me to go [with you(sg)] to your house and stay there [tonight]”!
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
So he came down quickly. [He took Jesus to his house] and welcomed him joyfully.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
The people [who saw Jesus go there] grumbled saying, “He has gone to be the guest of a man who is a sinner!”
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
Then Zacchaeus stood up [while they were eating] and said to the Lord [Jesus], “Lord, I want you [(sg)] to know that I am going to give half of what I own to poor people. And as for the people whom I have cheated, I will pay them back four times the amount [I have gotten from them by cheating].”
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
Jesus said to him, “Today [God] has forgiven [PRS] [you and the other people in] [MTY] this house, because you [(sg)] also [have shown that you have trusted in God as] your ancestor Abraham [did].
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
Remember this: [I], the one who came from heaven, came to seek and save [people like you(sg)] who have [gone astray from God, just like a shepherd who searches for his] lost [sheep].”
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
They were coming near to Jerusalem, and the people who were [going with Jesus] who heard him say these things thought that as soon as [he got to Jerusalem] he would become their king.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
[So] he told them this parable: “A prince prepared to go to a distant country in order that [the Emperor] would make him a king. [He intended] to return later.
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
[Before he left], he summoned ten of his servants. He gave each of them a coin worth three months’ wages. He said to them, ‘Do business with these coins until I return!’ [Then he left].
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
But [many of] his fellow-citizens hated him. So after he left they sent some messengers to tell [the Emperor], ‘We [(exc)] do not want this man to be our king!’
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
But [the Emperor] made him king anyway. [Later] the [new king] returned. Then he commanded that the servants to whom he had given the coins should be summoned {that someone should summon the servants to whom he had given the coins}. He wanted to know how much they had gained by doing business with the coins.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
The first man came [to him] and said, ‘Sir, with your one coin [I] have earned ten more [coins]!’
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
He said to this man, ‘[You are a] good servant! [You have] done [very] well! Because you have [handled] faithfully a small amount [of money, I will give you] authority [to rule] ten cities.’
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
Then the second servant came and said, ‘Sir, with your one coin [I] have earned five more [coins]!’
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
He said to that servant similarly, ‘[Good! I will give you authority to rule] five cities.’
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
Then another servant came. He said, ‘Sir, here is your coin. I wrapped it in a napkin and put it away, [so that nothing would happen to it].
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
I did that [because] I was afraid [of what you would do to me if the business failed. I know] you are a man who does not do foolish things with your money. You [even] take [from others money] that does not really belong to you, [like a farmer who] harvests grain [from another man’s field] where he did not [even] do the planting.’
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
The king said to that servant, ‘You wicked servant! I will condemn you by the very words [MTY] that you [have just now spoken]. (You know that I do not [do foolish things with my money]./Did you not know that I do not [do foolish things with my money]?) [RHQ] [You said] that I [even] take [from others money] that does not really [belong to me], [like a farmer who] harvests grain [from another man’s field] where he did not [even] do the planting.
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
So (you should at least have given my money to money lenders!/why did you not [at least] give my money to bankers?) [RHQ] Then [when I returned] I could have collected that amount plus the interest [it would have earned]!’
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
Then [the king] said to those who were standing near, ‘Take the coin from him and give it to [the servant] who has ten coins!’
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
They protested, ‘But Sir, he already has ten [coins]!’
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
[But the king said], ‘I tell you this: To the people who [use well what] they have [received], more will be given {[I] will give more}. But from the people who [do] not [use well what they have received], even what they [already] have will be taken away {[I] will take away even what they already have}.
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
Now, [as for] those enemies of mine who did not want me to rule over them, bring them here and execute them while I am watching!’”
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
After [Jesus] said those things, he [continued on the road] up to Jerusalem, going ahead of his disciples.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
When they got near Bethphage and Bethany [villages], near the hill that is called {that they call} Olive [Tree] Hill,
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
he said to two of [his] disciples, “Go to the village just ahead [of you]. As you [two] enter [it], you will see a young animal that no one has ever ridden, that has been {someone has} tied up. Untie it and bring it [to me].
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
If anyone asks you, ‘Why are you untying it?’ say [to him], ‘The Lord needs it.’”
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
[So] the [two disciples] went [to the village] and found the [animal], just like he had told them.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
As they were untying it, its owners said to them, “Why are you two untying that young animal?”
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
They replied, “The Lord needs it.” [So the owners said that they could take it].
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
The [two disciples] brought [the animal] to Jesus. They threw their cloaks on the animal’s back [for him to sit on] and helped Jesus get on it.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
Then as he rode along, [others] spread their cloaks on the road [to honor him].
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
As they came near [to Jerusalem], on the road that descends from Olive [Tree] Hill, the whole crowd of his disciples began to rejoice and praise God loudly for all the great miracles that they had seen [Jesus do].
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
They were saying things like, “May the Lord [God] bless our king who comes representing [MTY] him!” “May there be peace [between God] in heaven [and us his people]!” “May [everyone] praise God!”
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
Some of the Pharisees who were in the crowd said to Jesus, “Teacher, rebuke your disciples [for saying things like that]!”
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
He replied, “I tell you this: If these people would be silent, the stones themselves would shout [to praise me]!”
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
When [Jesus] came near [to] Jerusalem and saw the city, he cried about [its people].
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
He said, “[My disciples know what they need to do] to have peace [with God]; I wish that even today [the rest of] you people knew it. But now you are unable to know [MTY] it.
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
I want you to know this: Soon [your enemies] will come and will set up a barricade around your [city]. They will surround [the city] and attack [it] on all sides.
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
They will [break through] the walls [and] destroy everything. They will smash you and your people/children. [When they finish destroying everything], there will not be one stone left on top of another. [All this will happen] because you did not recognize the time when God sent his [Messiah] to [save] you!”
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
[Jesus entered Jerusalem and] went into the Temple [courtyard]. He saw the people who were selling [things there],
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
and he began to chase them out. He said to them, “It has been written {[A prophet] wrote} [in the Scriptures that God said], ‘[I want] my house to be a place where people pray’; but you bandits have made it a cave where you can [hide]!”
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
Each day [during that week Jesus] was teaching people in the Temple [courtyard]. The chief priests and the men who taught the [Jewish] laws and [other Jewish] leaders tried to find a way to kill him.
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
But they did not find any way to do it, because all the people there listened eagerly to him [and would have resisted them if they had tried to hurt him].

< Luka 19 >