< Luka 19 >
1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
He entered and started passing through Jericho.
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
A man named Zacchaeus was there—he was a chief tax collector, and he was wealthy!
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
He was trying to see who Jesus was, but could not because of the crowd, because he was short.
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
And running on ahead he climbed up into a sycamore tree, in order to see Him, since He was about to pass by there.
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
And when Jesus came to the place, He looked up and saw him, and said to him, “Zacchaeus, come down quickly, because today I must stay at your house.”
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
So he came down quickly, and received Him joyfully.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
But when they saw it, they all started complaining, saying, “He has entered to lodge with a sinful man!”
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
Then Zacchaeus stood and said to the Lord, “Indeed, Lord, I herewith give half of my goods to the poor, and if I have extorted anything from anyone, I restore fourfold.”
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
So Jesus said about him, “Today salvation has happened in this house, in that he also is a son of Abraham;
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
because the Son of the Man has come to seek and to save that which was lost.”
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
Now as they heard these things, He continued with a parable, because He was near Jerusalem and they were supposing that the Kingdom of God was on the verge of being revealed.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
So He said: “A certain nobleman went to a distant country to receive for himself a kingdom and return.
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
He called ten of his slaves, gave them ten ‘minas’, and said to them, ‘Conduct business until I come.’
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
But his citizens hated him and sent a delegation after him, saying, ‘We do not want this man to reign over us.’
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
It happened that he did receive the kingdom, and upon returning he ordered that those slaves to whom he had given the money be called to him, to know who had gained what by trading.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
So the first one came and said, ‘Master, your mina earned ten minas!’
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
He said to him: ‘Super, you good slave! Because you were faithful in a very little, have authority over ten cities!’
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
And the second one came and said, ‘Master, your mina made five minas.’
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
Likewise he said to him, ‘You also be over five cities.’
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
Then a different one came, saying: ‘Master, here is your mina, that I kept laid away in a piece of cloth
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
—I feared you because you are a hard man, removing what you did not place, and reaping what you did not sow.’
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
So he said to him: ‘I will judge you out of your own mouth, you wicked slave! You knew that I am a hard man, removing what I did not place, and reaping what I did not sow.
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
Why then didn't you put my money on deposit, and upon coming I would have collected it with interest?’
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
And to those standing by he said, ‘Take the mina from him and give it to him who has the ten minas.’
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
(They even said to him, ‘Master, he already has ten minas!’)
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
‘Indeed I tell you, to everyone who has, more will be given; but from him who does not have, even what he has will be taken from him.
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
But as for those enemies of mine who did not want me to reign over them, bring them here and slaughter them in front of me!’”
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
Having said these things, He went on ahead, going up to Jerusalem.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
When He drew near to Bethphage and Bethany, at the mountain called ‘of Olives’, it happened like this: He sent two of His disciples,
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
saying: “Go to the village opposite you, where as you enter you will find a colt tied, on which no man ever yet sat. Untie and bring it.
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
And if anyone asks you, ‘Why are you untying it?’ just say this to him: ‘The Lord needs it.’”
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
So those who were sent went and found it just like He told them.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
As they were untying the colt, its owners said to them, “Why are you untying the colt?”
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
So they said, “The Lord needs it.”
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
Then they brought it to Jesus; and throwing their own clothes on the colt, they placed Jesus on it.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
And as He went along people were spreading their clothes on the road.
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
Then, as He was approaching the descent of the Mount of Olives, the whole multitude of the disciples began to rejoice and praise God with a loud voice for all the mighty works they had seen,
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
saying: “Blessed is the King who comes in the name of the Lord! Peace in heaven and glory in the highest!”
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
Some of the Pharisees said to Him from the crowd, “Teacher, rebuke your disciples!”
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
In answer He said to them, “I tell you that if these should keep silent, the very stones would cry out!”
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
Now as He approached, observing the city He wept over it,
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
saying: “If you, yes you, especially in this your day, had known the things pertaining to your peace! But now they are hidden from your eyes.
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
Yes, the days will come upon you when your enemies will build an embankment around you; indeed they will surround you and hem you in on every side.
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
And they will raze you, and your children within you, to the ground—they will not leave in you one stone upon another—all because you did not recognize the time of your visitation.”
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
And upon entering the temple He began to drive out those who were selling and buying in it,
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
saying to them, “It is written: ‘My house is a house of prayer,’ but you have made it a ‘den of robbers’!”
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
And He was teaching daily in the temple; but the chief priests and the scribes, as also the leaders of the people, were trying to destroy Him,
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
but could not figure out how to do it, because all the people were hanging on His words.