< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
Og han kom ind i Jeriko og drog derigennem.
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
Og se, der var en Mand, som hed Zakæus; han var Overtolder, og han var rig.
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
Og han søgte at få at se, hvem der var Jesus, og kunde ikke for Skaren, fordi han var lille af Vækst.
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
Og han løb forud og steg op i et Morbær Figentræ, for at han kunde se ham; thi han skulde komme frem ad den Vej.
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
Og da Jesus kom til Stedet, så han op og blev ham var og sagde til ham: "Zakæus! skynd dig og stig ned; thi jeg skal i Dag blive i dit Hus."
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
Og han skyndte sig og steg ned og tog imod ham med Glæde.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
Og da de så det, knurrede de alle og sagde: "Han er gået ind for at tage Herberge hos en syndig Mand."
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
Men Zakæus stod frem og sagde til Herren: "Se, Herre! Halvdelen af min Ejendom giver jeg de fattige; og dersom jeg har besveget nogen for noget, da giver jeg det fire Fold igen."
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
Men Jesus sagde til ham: "I Dag er der blevet dette Hus Frelse til Del, efterdi også han er en Abrahams Søn;
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
thi Menneskesønnen er kommen for at søge og frelse det fortabte."
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
Men medens de hørte på dette, fortsatte han og sagde en Lignelse, fordi han var nær ved Jerusalem, og de mente, at Guds Rige skulde straks komme til Syne.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
Han sagde da: "En højbåren Mand drog til et fjernt Land for at få Kongemagt og vende tilbage igen.
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
Men han kaldte ti af sine Tjenere og gav dem ti Pund og sagde til dem: Købslår dermed, indtil jeg kommer.
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
Men hans Medborgere hadede ham og skikkede Sendebud efter ham og lod sige: Vi ville ikke, at denne skal være Konge over os.
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
Og det skete, da han kom igen, efter at han havde fået Kongemagten, sagde han, at disse Tjenere, hvem han havde givet Pengene, skulde kaldes for ham, for at han kunde få at vide, hvad hver havde vundet.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
Og den første trådte frem og sagde: Herre! dit Pund har erhvervet ti Pund til.
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
Og han sagde til ham: Vel, du gode Tjener! efterdi du har været tro i det mindste, skal du have Magt over ti Byer.
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
Og den anden kom og sagde: Herre! dit Pund har indbragt fem Pund.
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
Men han sagde også til denne: Og du skal være over fem Byer.
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
Og en anden kom og sagde: Herre! se, her er dit Pund, som jeg har haft liggende i et Tørklæde.
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
Thi jeg frygtede for dig, efterdi du er en streng Mand; du tager, hvad du ikke lagde, og høster, hvad du ikke såede.
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
Han siger til ham: Efter din egen Mund dømmer jeg dig, du onde Tjener! Du vidste, at jeg er en streng Mand, som tager, hvad jeg ikke lagde, og høster, hvad jeg ikke såede;
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
hvorfor gav du da ikke mine Penge til Vekselbordet, så jeg ved min Hjemkomst kunde have krævet dem med Rente?
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
Og han sagde til dem, som stode hos: Tager Pundet fra ham, og giver det til ham, som har de ti Pund.
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
Og de sagde til ham: Herre! han har ti Pund.
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
Jeg siger eder, at enhver, som har, ham skal der gives; men den, som ikke har, fra ham skal endog det tages, som han har.
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
Men fører disse mine Fjender hid, som ikke vilde, at jeg skulde være Konge over dem, og hugger dem ned for mine Øjne!"
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
Og da han havde sagt dette, gik han foran og drog op til Jerusalem.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
Og det skete, da han nærmede sig til Bethfage og Bethania ved det Bjerg, som kaldes Oliebjerget, udsendte han to af sine Disciple og sagde:
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
"Går hen til den Landsby, som ligger lige for eder. Når I komme derind, skulle I finde et Føl bundet, på hvilket der endnu aldrig har siddet noget Menneske; og løser det, og fører det hid!
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
Og dersom nogen spørger eder: Hvorfor løse I det? da skulle I sige således: Herren har Brug for det."
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
Men de udsendte gik hen og fandt det, ligesom han havde sagt dem.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
Men da de løste Føllet, sagde dets Herrer til dem: "Hvorfor løse I Føllet?"
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
Og de sagde: "Herren har Brug for det."
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
Og de førte det til Jesus, og de lagde deres Klæder på Føllet og lod Jesus sætte sig derpå.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
Og da han drog frem, bredte de deres Klæder under ham på Vejen.
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
Men da han nu nærmede sig til Nedgangen fra Oliebjerget, begyndte hele Disciplenes Mængde med Glæde at prise Gud med høj Røst for alle de kraftige Gerninger, som de havde set, og de sagde:
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
"Velsignet være Kongen, som kommer, i Herrens Navn! Fred i Himmelen, og Ære i det højeste!"
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
Og nogle af Farisæerne i Skaren sagde til ham: "Mester! irettesæt dine Disciple!"
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
Og han svarede og sagde til dem: "Jeg siger eder, at hvis disse tie, skulle Stenene råbe."
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
Og da han kom nær til og så Staden, græd han over den og sagde:
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
"Vidste dog også du, ja, selv på denne din Dag, hvad der tjener til din Fred! Men nu er det skjult for dine Øjne.
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
Thi der skal komme Dage over dig, da dine Fjender skulle kaste en Vold op omkring dig og omringe dig og trænge dig alle Vegne fra;
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
og de skulle lægge dig helt øde og dine Børn i dig og ikke lade Sten på Sten tilbage i dig, fordi du ikke kendte din Besøgelses Tid."
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
Og han gik ind i Helligdommen og begyndte at uddrive dem, som solgte,
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
og sagde til dem: "Der er skrevet: Og mit Hus er et Bedehus; men I have gjort det til en Røverkule."
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
Og han lærte daglig i Helligdommen; men Ypperstepræsterne og de skriftkloge og de første i Folket søgte at slå ham ihjel.
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
Og de fandt ikke, hvad de skulde gøre; thi hele Folket hang ved ham og hørte ham.

< Luka 19 >