< Luka 19 >
1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
耶稣走进耶利哥城,穿城而过。
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
有一个名叫撒该的税吏长,非常富有。
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
他想看看耶稣到底是谁,但在人群中,身材矮小的他无法看见。
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
于是他跑到前面,爬上一棵无花果树,想在耶稣经过的时候看看他的样子。
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
耶稣走到这里后往上一看,对他说:“撒该,快下来,今天我要住在你家中。”
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
撒该马上爬下来,高兴地迎接耶稣到他家去。
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
众人见状议论纷纷:“他竟要住在这样的罪人家中!”
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
撒该站着对主说:“主啊,你看,我正在把一半的家财分给穷人,如果我曾欺骗谁,就会四倍奉还!”
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
耶稣说:“今天这栋房子迎来了救赎,他也是亚伯拉罕的子孙。
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
因为人子来寻找和拯救的就是迷失之人。”
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
众人专心听着耶稣的话。由于这里接近耶路撒冷,加上民众都认为上帝之国即将出现,于是耶稣就讲了一个故事。
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
他说:“从前有一个贵族,他离开家去远方接受王位加冕,然后再回到家。
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
他叫了自己的十个仆人来,将钱平分给他们,然后说:‘你们用这钱去做投资,一直到我回来。’
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
但这国家的人都憎恨他,于是派一个代表跟过去,说:‘我们不想这个人做王统治我们。’
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
贵族获得王位后返回,然后将那些拿钱投资的仆人召来,询问他们做投资的收益情况。
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
第一个仆人上前说:‘主人,你的钱已经赚了十倍。’
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
国王说:‘做得好,你是个好仆人,因为你证明了在小事上很忠心,我现在派你去管理十座城。’
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
第二个过来说:‘主人,你的钱已经赚了五倍。’
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
国王说:‘我派你去管理五座城。’
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
另一个仆人走进来说:‘主啊,你看,这是你的钱,现在还给你。我用布包着它,确保安全。
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
你是个严厉的人,我很害怕你。我怕你会拿走不属于你的东西,会收走你没有种下的作物。’
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
国王回答:‘我要根据你这番话来审判你。你知道我很严厉,会拿走不属于我的东西,会收走我没有种下的作物。
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
那你为什么不把我的钱存入银行,等我回来的时候,就可以连本带息取回来?’
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
国王对身边站着的仆人说:‘把他的钱拿走,交给那赚了十倍的人。’
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
侍卫说:‘但主人,他已经有了十倍的钱了。’
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
国王说:‘告诉你们吧,那些已经有的,还会有更多。没有的,现在有的也会被拿走。
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
至于那些不愿意我做国王统治他们的敌人,现在把他们拉到这里来,当着我的面杀掉!’”
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
耶稣讲完这个故事,就继续向前朝着耶路撒冷走去。
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
快到伯法其和伯大尼时,他来到了橄榄山,在那里叫来两名门徒,对他们说:
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
“你们到前面的村子去,进去后会看见有一个地方拴着一头从未有人骑过的小驴,解开它的绳子,把它牵来。
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
如果有人问为什么解开它,你们就说:‘主需要它。’”
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
两名门徒出发了,后来发生的一切与耶稣所说如出一辙。
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
他们解开小驴的时候,驴主人问:“你们为什么解开它?”
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
他们说:“主需要它。”
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
门徒把小驴牵到耶稣那里,把自己的衣服搭在驴背上,耶稣坐在上面。
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
耶稣骑驴前行,众人把自己的衣服铺在路上。
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
当他走近耶路撒冷,这里也是橄榄山的下山路,门徒们因为看见了所有神迹,开始充满喜悦地大声赞美上帝。
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
他们大声喊:“奉主之名前来的王,赞颂你!愿和平降临天堂,愿荣耀降临至高天堂!”
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
民众中有几个法利赛人对他说:“老师,不要让你的门徒说这些!”
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
耶稣说:“我告诉你们,他们若保持沉默,石头就要呼喊了!”
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
耶路撒冷越来越近了,耶稣看见这座城,开始为之哭泣,
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
他说:“我真希望你们——就是你们啊,在今天能知道通往平安的路,但都隐藏起来了,你们看不到。
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
时间一到,你们的仇敌就会包围过来,搭建斜坡攻击你们,把你们团团围住,困住你们,
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
他们会彻底摧毁你们,还有你们的孩子。所有的石头建筑都会轰然倒塌,因为你们在救赎到来之刻拒绝接受。”
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
耶稣走进神庙,赶走做买卖之人,
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
他对他们说:“经文上记着:‘我的殿将用于祷告’。你们却把它变成贼窝了。”
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
然后他每天都在神庙里教导众人。祭司长、宗教老师和首领都想杀害他,
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
但又不知道如何下手,因为众人都围着他并聆听。