< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
He also taught them by a parable that they must always pray and never lose heart.
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
"In a certain town," He said, "there was a judge who had no fear of God and no respect for man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
And in the same town was a widow who repeatedly came and entreated him, saying, "'Give me justice and stop my oppressor.'
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
"For a time he would not, but afterwards he said to himself, "'Though I have neither reverence for God nor respect for man,
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
yet because she annoys me I will give her justice, to prevent her from constantly coming to pester me.'"
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
And the Lord said, "Hear those words of the unjust judge.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
And will not God avenge the wrongs of His own People who cry aloud to Him day and night, although He seems slow in taking action on their behalf?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
Yes, He will soon avenge their wrongs. Yet, when the Son of Man comes, will He find faith on earth?"
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
And to some who relied on themselves as being righteous men, and looked down upon all others, He addressed this parable.
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
"Two men went up to the Temple to pray," He said; "one being a Pharisee and the other a tax-gatherer.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
The Pharisee, standing erect, prayed as follows by himself: "'O God, I thank Thee that I am not like other people--I am not a thief nor a cheat nor an adulterer, nor do I even resemble this tax-gatherer.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twice a week. I pay the tithe on all my gains.'
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
"But the tax-gatherer, standing far back, would not so much as lift his eyes to Heaven, but kept beating his breast and saying, "'O God, be reconciled to me, sinner that I am.'
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
"I tell you that this man went home more thoroughly absolved from guilt than the other; for every one who uplifts himself will be humbled, but he who humbles himself will be uplifted."
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
On one occasion people also brought with them their infants, for Him to touch them; but the disciples, noticing this, proceeded to find fault with them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
Jesus however called the infants to Him. "Let the little children come to me," He said; "do not hinder them; for it is to those who are childlike that the Kingdom of God belongs.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
I tell you in solemn truth that, whoever does not receive the Kingdom of God like a little child will certainly not enter it."
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
The question was put to Him by a Ruler: "Good Rabbi, what shall I do to inherit the Life of the Ages?" (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
"Why do you call me good?" replied Jesus; "there is no one good but One, namely God.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
You know the Commandments: 'Do not commit adultery;' 'Do not murder;' 'Do not steal;' 'Do not lie in giving evidence;' 'Honour thy father and thy mother.'"
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
"All of those," he replied, "I have kept from my youth."
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
On receiving this answer Jesus said to him, "There is still one thing wanting in you. Sell everything you possess and give the money to the poor, and you shall have wealth in Heaven; and then come, follow me."
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
But on hearing these words he was deeply sorrowful, for he was exceedingly rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
Jesus saw his sorrow, and said, "With how hard a struggle do the possessors of riches ever enter the Kingdom of God!
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Why, it is easier for a camel to go through a needle's eye than for a rich man to enter the Kingdom of God."
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
"Who then can be saved?" exclaimed the hearers.
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
"Things impossible with man," He replied, "are possible with God."
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
Then Peter said, "See, we have given up our homes and have followed you."
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
"I solemnly tell you," replied Jesus, "that there is no one who has left house or wife, or brothers or parents or children, for the sake of God's Kingdom,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who shall not certainly receive many times as much in this life, and in the age that is coming the Life of the Ages." (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
Then He drew the Twelve to Him and said, "See, we are going up to Jerusalem, and everything written in the Prophets which refers to the Son of Man will be fulfilled.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
For He will be given up to the Gentiles, and be mocked, outraged and spit upon.
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
They will scourge Him and put Him to death, and on the third day He will rise to life again."
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
Nothing of this did they understand. The words were a mystery to them, nor could they see what He meant.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
As Jesus came near to Jericho, there was a blind man sitting by the way-side begging.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
He heard a crowd of people going past, and inquired what it all meant.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
"Jesus the Nazarene is passing by," they told him.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Then, at the top of his voice, he cried out, "Jesus, son of David, take pity on me."
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Those in front reproved him and tried to silence him; but he continued shouting, louder than ever, "Son of David, take pity on me."
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
At length Jesus stopped and desired them to bring the man to Him; and when he had come close to Him He asked him,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
"What shall I do for you?" "Sir," he replied, "let me recover my sight."
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
"Recover your sight," said Jesus: "your faith has cured you."
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
No sooner were the words spoken than the man regained his sight and followed Jesus, giving glory to God; and all the people, seeing it, gave praise to God.

< Luka 18 >