< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
And He spoke a parable to them that it behooves them to pray always, and not to faint;
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
saying, There was a certain judge in a certain city, fearing not God, and regarding not man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
And there was a widow in that city; and she continued to come to him, saying, Avenge me of mine adversary.
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
And he was not willing for a time: but after these things he said in himself, Though I fear not God nor regard man,
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
yet because this widow causes me trouble, I will avenge her, lest coming forever she may smite me in the face.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
But the Lord said, I fear what the unjust judge says.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
And shall not God avenge His elect, crying to Him day and night, and He is long-suffering over them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
I say unto you, that He will avenge them speedily. Moreover the Son of man having come, will He then find faith upon the earth?
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
And He spoke this parable to certain ones having confidence in themselves that they are righteous, and despising the rest.
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
Two men went up into the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
The Pharisee standing was praying in these words, God, I thank thee because I am not like the rest of the men, extortioners, unjust, adulterous, or even as this publican:
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twice per week; I give tithes of all things so many as I possess.
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
But the publican, standing a great way off, did not wish even to lift up his eyes to the heaven, but smote upon his breast, saying, God, be merciful to me the sinner.
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
I say unto you, He went down to his house justified rather than the other: because every one exalting himself shall be abased; and the one humbling himself shall be exalted.
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
And they were indeed bringing the infants to Him, that He should touch them: but the disciples seeing rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
And Jesus calling them to Him, said, Suffer the little children to come unto me, and forbid them not: for of such is the kingdom of God.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Truly I say unto you, whosoever may not receive the kingdom of God as a little child, can not enter into it.
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
And a certain ruler asked Him, saying, Good Teacher, having done what, shall I inherit eternal life? (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
And Jesus said to him, Why do you call me good? No one is good, except One, God.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
You know the commandments, thou must not commit adultery, thou must not murder, thou must not steal, thou must not bear false witness, honor thy father and mother.
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
And he said, All these things have I kept from my youth.
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
And Jesus hearing these things, said to him, Still one thing is lacking to thee: Sell all things whatsoever you have, and give to the poor, and you shall have treasure in heaven: and come, follow me.
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
And hearing these things, he went away very sorrowful; for he was exceedingly rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
Jesus seeing him said, How hardly will those having riches enter into the kingdom of God!
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
For it is easier for a camel to go through the eye of a needle, than for a rich man to go into the kingdom of God.
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
And those hearing said, And who is able to be saved?
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
And He said, Those things which are impossible with men are possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
And Peter said, Behold, we have left all things, and followed thee.
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And He said to them, Truly I say unto you, that there is no one who has left house, or parents, or brothers, or wife, or children, for the sake of the kingdom of God,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who may not receive a hundredfold in this time, and in the coming age eternal life. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
And taking the twelve aside, He said to them, Behold, we go up to Jerusalem, and all things which have been written by the prophets shall be perfected to the Son of man.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
For He will be delivered to the Gentiles; and be mocked, and insulted, and spat upon:
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
and having scourged Him, they will kill Him; and He will arise the third day.
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
And they understood none of these things; and this word was hidden from them, and they did not know the things spoken.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
And it came to pass, while He was drawing nigh to Jericho, a certain blind man was sitting by the wayside begging.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
And hearing the multitude passing by, he inquired what it might be.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
And they told him that Jesus the Nazarene is going along.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And he cried out saying, Jesus, thou son of David, have mercy on me.
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And the passersby continued to rebuke him, that he should keep silent: but he continued to cry out much more, O thou son of David, have mercy on me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
And Jesus standing, commanded him to be led to Him; and he drawing nigh, He asked him,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
What do you wish that I shall do to you? And he said, Lord, that I may look up.
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him, Look up: thy faith hath saved thee.
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
And immediately he looked up, and followed Him, glorifying God: and all the people, seeing, gave praise to God.

< Luka 18 >