< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
Now he also told them a parable, that we should continually pray and not cease,
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
saying: “There was a certain judge in a certain city, who did not fear God and did not respect man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
But there was a certain widow in that city, and she went to him, saying, ‘Vindicate me from my adversary.’
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
And he refused to do so for a long time. But afterwards, he said within himself: ‘Even though I do not fear God, nor respect man,
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
yet because this widow is pestering me, I will vindicate her, lest by returning, she may, in the end, wear me out.’”
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
Then the Lord said: “Listen to what the unjust judge said.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
So then, will not God grant the vindication of his elect, who cry out to him day and night? Or will he continue to endure them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
I tell you that he will quickly bring vindication to them. Yet truly, when the Son of man returns, do you think that he will find faith on earth?”
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
Now about certain persons who consider themselves to be just, while disdaining others, he told also this parable:
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
“Two men ascended to the temple, in order to pray. One was a Pharisee, and the other was a tax collector.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
Standing, the Pharisee prayed within himself in this way: ‘O God, I give thanks to you that I am not like the rest of men: robbers, unjust, adulterers, even as this tax collector chooses to be.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twice between Sabbaths. I give tithes from all that I possess.’
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
And the tax collector, standing at a distance, was not willing to even lift up his eyes to heaven. But he struck his chest, saying: ‘O God, be merciful to me, a sinner.’
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
I say to you, this one descended to his house justified, but not the other. For everyone who exalts himself will be humbled; and whoever humbles himself will be exalted.”
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
And they were bringing little children to him, so that he might touch them. And when the disciples saw this, they rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
But Jesus, calling them together, said: “Allow the children to come to me, and do not be an obstacle to them. For of such is the kingdom of God.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Amen, I say to you, whoever will not accept the kingdom of God like a child, will not enter into it.”
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
And a certain leader questioned him, saying: “Good teacher, what should I do to possess eternal life?” (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
Then Jesus said to him: “Why do you call me good? No one is good except God alone.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
You know the commandments: You shall not kill. You shall not commit adultery. You shall not steal. You shall not give false testimony. Honor your father and mother.”
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
And he said, “I have kept all these things from my youth.”
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
And when Jesus heard this, he said to him: “One thing is still lacking for you. Sell all the things that you have, and give to the poor. And then you will have treasure in heaven. And come, follow me.”
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
When he heard this, he became very sorrowful. For he was very rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
Then Jesus, seeing him brought to sorrow, said: “How difficult it is for those who have money to enter into the kingdom of God!
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
For it is easier for a camel to pass through the eye of a needle, than for a wealthy man to enter into the kingdom of God.”
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
And those who were listening to this said, “Then who is able to be saved?”
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
He said to them, “Things that are impossible with men are possible with God.”
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
And Peter said, “Behold, we have left everything, and we have followed you.”
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And he said to them: “Amen, I say to you, there is no one who has left behind home, or parents, or brothers, or a wife, or children, for the sake of the kingdom of God,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who will not receive much more in this time, and in the age to come eternal life.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
Then Jesus took the twelve aside, and he said to them: “Behold, we are ascending to Jerusalem, and everything shall be completed which was written by the prophets about the Son of man.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
For he will be handed over to the Gentiles, and he will be mocked and scourged and spit upon.
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
And after they have scourged him, they will kill him. And on the third day, he will rise again.”
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
But they understood none of these things. For this word was concealed from them, and they did not understand the things that were said.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
Now it happened that, as he was approaching Jericho, a certain blind man was sitting beside the way, begging.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
And when he heard the multitude passing by, he asked what this was.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
And they told him that Jesus of Nazareth was passing by.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And he cried out, saying, “Jesus, Son of David, take pity on me!”
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And those who were passing by rebuked him, so that he would be silent. Yet truly, he cried out all the more, “Son of David, take pity on me!”
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
Then Jesus, standing still, ordered him to be brought to him. And when he had drawn near, he questioned him,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
saying, “What do you want, that I might do for you?” So he said, “Lord, that I may see.”
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him: “Look around. Your faith has saved you.”
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
And immediately he saw. And he followed him, magnifying God. And all the people, when they saw this, gave praise to God.

< Luka 18 >