< Luka 17 >
1 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
Then he said to his disciples: It is impossible that causes of offense should not come; but alas for him by whom they come!
2 Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
It would be better for him that a millstone were hung about his neck, and he were thrown into the sea, than that he should cause one of these little ones to sin.
3 Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
Take heed to yourselves; if your brother sin against you, rebuke him; and if he repent, forgive him.
4 Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
And if he sin against you seven times in a day, and seven times in a day turn again to you and say, I repent, you shall forgive him.
5 Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
And the apostles said to the Lord: Increase our faith.
6 Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
And the Lord said: If you had faith like a grain of mustard, you might say to this sycamine-tree, Be uprooted, and be planted in the sea, and it should obey you.
7 Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
Which of you that has a servant plowing, or feeding a flock, will say to him immediately, when he comes in from the field, Go and recline at table?
8 Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
But will he not say to him, Make ready my supper, and gird yourself, and serve me, till I have eaten and drunk; and afterward, you shall eat and drink?
9 Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
Does he thank that servant, because he did what was commanded? I think not.
10 Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
So also you, when you shall have done all things that you arc commanded to do, say, We are unprofitable servants; for we have done what was our duty to do.
11 Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
And it came to pass, as he was journeying to Jerusalem, that he passed through the midst of Samaria and Galilee.
12 Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
And as he entered a certain village, there met him ten men that were lepers, who stood at a distance.
13 sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
And they lifted up their voice, saying: Jesus, Master, have mercy on us.
14 Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
And when he saw them, he said to them: Go, show yourselves to the priests. And it came to pass, that, as they went, they were made clean.
15 Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
But, one of them, seeing that he was restored to health, turned back, and, with a loud voice, glorified God.
16 Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
And he fell on his face at his feet, and gave him thanks; and he was a Samaritan.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
And Jesus answered and said: Were not the ten cleansed? but where are the nine?
18 Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
Were there none found to return and give glory to God, but this one of another race?
19 Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And he said to him: Arise, and go; your faith has saved you.
20 Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
And being asked by the Pharisees, when the kingdom of God should come, he answered them and said: The kingdom of God comes not so as to attract attention;
21 Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
nor shall it be said, Lo here! or Lo there! for, behold, the kingdom of God is among you.
22 Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
And he said to his disciples: The days will come, when you will desire to see one of the days of the Son of man, and shall not see it.
23 Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
And they shall say to you, Lo here! or Lo there! go not after them, nor follow them.
24 Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
For as the lightning that flashes out of one part under heaven, shines to another part under heaven, so shall the Son of man be in his day.
25 Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
But first he must suffer many things, and be rejected by this generation.
26 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
And as it was in the days of Noah, so shall it be also in the days of the Son of man.
27 Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
They ate, they drank, they married, they were given in marriage, till the day in which Noah entered the ark, and the flood came and destroyed them all.
28 Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
In like manner also, as it was in the days of Lot: they ate, they drank, they bought, they sold, they planted, they builded;
29 Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
but in the day in which Lot went out of Sodom, it rained fire and brimstone from heaven, and destroyed them all.
30 Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
Even thus shall it be in the day in which the Son of man is revealed.
31 A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
In that day, let not him that is on the house-top, and whose goods are in the house, come down to take them away. Likewise, he that is in the field, let him not turn back.
32 Ku tuna fa da matar Lutu.
Remember Lot’s wife.
33 Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
Whoever will seek to save his life, shall lose it; and whoever will lose his life, shall save it.
34 Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
I say to you, on that night two men shall be in one bed; the one shall be taken, and the other left.
35 Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
Two women shall be grinding together; the one shall be taken, and the other left.
36 [“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
Two men shall be in the field; the one shall be taken, and the other left.
37 Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”
And they answered and said to him. Where, Lord? And he said to them: Where the body is, there will the vultures be gathered.