< Luka 16 >
1 Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
He said also to His disciples: "There was a rich man who had a steward, about whom a report was brought to him, that he was wasting his property.
2 Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
He called him and said, "'What is this I hear about you? Render an account of your stewardship, for I cannot let you hold it any longer.'
3 Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
"Then the steward said within himself, "'What am I to do? For my master is taking away the stewardship from me. I am not strong enough for field labour: to beg, I should be ashamed.
4 Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
I see what to do, in order that when I am discharged from the stewardship they may give me a home in their own houses.'
5 Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
"So he called all his master's debtors, one by one, and asked the first, 'How much are you in debt to my master?'
6 Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
"'A hundred firkins of oil,' he replied. "'Here is your account,' said the steward: 'sit down quickly and change it into fifty firkins.'
7 Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
"To a second he said, "'And how much do you owe?' "'A hundred quarters of wheat,' was the answer. "'Here is your account,' said he: 'change it into eighty quarters.'
8 Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn )
"And the master praised the dishonest steward for his shrewdness; for, in relation to their own contemporaries, the men of this age are shrewder than the sons of Light. (aiōn )
9 Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios )
"But I charge you, so to use the wealth which is ever tempting to dishonesty as to win friends who, when it fails, shall welcome you to the tents that never perish. (aiōnios )
10 Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
The man who is honest in a very small matter is honest in a great one also; and he who is dishonest in a very small matter is dishonest in a great one also.
11 Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
If therefore you have not proved yourselves faithful in dealing with the wealth that is tainted with fraud, who will entrust to you the true good?
12 Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
And if you have not been faithful in dealing with that which is not your own, who will give you that which is your own?
13 Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
"No servant can be in bondage to two masters. For either he will hate one and love the other, or else he will cling fast to one and scorn the other. You cannot be bondservants both of God and of gold."
14 Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
To all this the Pharisees listened, bitterly jeering at Him; for they were lovers of money.
15 Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
"You are they," He said to them, "who boast of their own goodness before men, but God sees your hearts; for that which holds a proud position among men is detestable in God's sight.
16 Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
The Law and the Prophets continued until John came: from that time the Good News of the Kingdom of God has been spreading, and all classes have been forcing their way into it.
17 Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
But it is easier for earth and sky to pass away than for one smallest detail of the Law to fall to the ground.
18 Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
Every man who divorces his wife and marries another commits adultery; and he who marries her when so divorced from her husband commits adultery.
19 Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
"There was once a rich man who habitually arrayed himself in purple and fine linen, and enjoyed a splendid banquet every day,
20 Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
while at his outer door there lay a beggar, Lazarus by name,
21 Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
covered with sores and longing to make a full meal off the scraps flung on the floor from the rich man's table. Nay, the dogs, too, used to come and lick his sores.
22 Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
"But in course of time the beggar died; and he was carried by the angels into Abraham's bosom. The rich man also died, and had a funeral.
23 yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs )
And in Hades, being in torment, he looked and saw Abraham in the far distance, and Lazarus resting in his arms. (Hadēs )
24 Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
So he cried aloud, and said, "'Father Abraham, take pity on me and send Lazarus to dip the tip of his finger in water and cool my tongue, for I am in agony in this flame.'
25 Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
"'Remember, my child,' said Abraham, 'that you had all your good things during your lifetime, and that Lazarus in like manner had his bad things. But, now and here, he is receiving consolation and you are in agony.
26 Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
And, besides all this, a vast chasm is immovably fixed between us and you, put there in order that those who desire to cross from this side to you may not be able, nor any be able to cross over from your side to us.'
27 Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
"'I entreat you then, father,' said he, 'to send him to my father's house.
28 domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
For I have five brothers. Let him earnestly warn them, lest they also come to this place of torment.'
29 Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
"'They have Moses and the Prophets,' replied Abraham; 'let them hear them.'
30 Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
"'No, father Abraham,' he pleaded; 'but if some one goes to them from the dead, they will repent.'
31 Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”
"'If they are deaf to Moses and the Prophets,' replied Abraham, 'they would not be led to believe even if some one should rise from the dead.'"