< Luka 16 >

1 Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
Then Jesus said to his disciples, “There was a rich man whose steward was accused of squandering his possessions.
2 Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
So he called the steward in and said to him, ‘What is this I hear about yoʋ? Give an account of yoʋr stewardship, for yoʋ can no longer be steward.’
3 Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
The steward said to himself, ‘What should I do, now that my master is taking my stewardship away from me? I am not strong enough to dig, and I am ashamed to beg.
4 Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
I know what I will do so that, when I am removed from my stewardship, people will receive me into their homes.’
5 Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
So he summoned each one of his master's debtors. He said to the first, ‘How much do yoʋ owe my master?’
6 Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
The man said, ‘A hundred measures of oil.’ The steward said to him, ‘Take yoʋr bill, sit down quickly, and write fifty.’
7 Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
Then he said to another, ‘And how much do yoʋ owe?’ The man said, ‘A hundred measures of wheat.’ The steward said to him, ‘Take yoʋr bill and write eighty.’
8 Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
So the master commended the unrighteous steward because he had acted shrewdly. For the people of this world are more shrewd in dealing with their own generation than are the people of the light. (aiōn g165)
9 Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
And I tell you, make friends for yourselves by means of unrighteous wealth so that when you die, those friends will receive you into eternal dwellings. (aiōnios g166)
10 Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
“He who is faithful with very little is also faithful with much, and he who is dishonest with very little is also dishonest with much.
11 Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
If then you have not been faithful with unrighteous wealth, who will entrust you with true riches?
12 Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
And if you have not been faithful with the property of another, who will give you property of your own?
13 Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
No servant can serve two masters, for either he will hate one and love the other, or he will be devoted to one and despise the other. You cannot serve God and money.”
14 Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
Now the Pharisees, who were lovers of money, heard all these things and began ridiculing Jesus.
15 Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
So he said to them, “You present yourselves as righteous in the sight of men, but God knows your hearts. For what is highly esteemed among men is an abomination in the sight of God.
16 Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
“The Law and the Prophets were proclaimed until John; since then the good news of the kingdom of God has been preached, and everyone tries to force their way into it.
17 Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
But it is easier for heaven and earth to pass away than for one stroke of a letter to be dropped from the law.
18 Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
“For example, any man who divorces his wife and marries another commits adultery, and any man who marries a woman divorced from her husband commits adultery.
19 Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
“Now there was a certain rich man who would dress in purple and fine linen, enjoying himself each day as he lived lavishly.
20 Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
There was also a poor man named Lazarus, who was laid at the rich man's gate, covered with sores.
21 Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
He longed to be filled with the crumbs that fell from the rich man's table, but instead the dogs would come and lick his sores.
22 Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
Now the poor man died and was carried away by the angels to Abraham's side, and the rich man also died and was buried.
23 yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
As he was in torment in Hades, he lifted up his eyes and saw Abraham far off, and Lazarus at his side. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
So he called out and said, ‘Father Abraham, have mercy on me and send Lazarus to dip the tip of his finger in water and cool my tongue, for I am in agony in these flames.’
25 Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
But Abraham said, ‘Son, remember that in yoʋr lifetime yoʋ received yoʋr good things, and in the same way Lazarus received bad things, but now he is here being comforted, while yoʋ are in agony.
26 Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
And besides all this, a great chasm has been set in place between you and us, so that those who want to cross over to you from here cannot do so, nor can anyone cross over to us from there.’
27 Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
The rich man said, ‘Then I beg yoʋ, father, to send Lazarus to my father's house,
28 domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
for I have five brothers. Let him warn them, so that they will not also come to this place of torment.’
29 Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
Abraham said to him, ‘They have Moses and the Prophets; they can listen to them.’
30 Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
He said, ‘No, father Abraham, but if someone goes to them from the dead, they will repent.’
31 Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”
But Abraham said to him, ‘If they do not listen to Moses and the Prophets, neither will they be persuaded even if someone rises from the dead.’”

< Luka 16 >