< Luka 13 >
1 A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
Some people who were [listening to Jesus] at that time told him about some people from Galilee [district who had gone to Jerusalem]. Pilate, [the Roman governor], had [ordered soldiers to] kill them [MTY] while they were offering sacrifices [in the Temple there].
2 Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
Jesus replied to them, “Do you think [that this happened to those] people from Galilee [because] they were more sinful than all the other people from Galilee?
3 A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
I assure you, [that was] not [so]! But instead of [being concerned about them, you need to remember that God] will similarly punish you [eternally] if you do not turn away from your sinful behavior.
4 Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Or, [consider] the 18 people who died when the tower at Siloam [outside Jerusalem] fell on them. Do you think [that this happened to them because] they were more sinful than all the other people who lived in Jerusalem?
5 Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
I assure you, [that was] not so! But instead, you [need to realize that God] will similarly punish you [eternally] if you do not stop your sinful behavior!”
6 Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
Then Jesus told them this illustration [to show what God would do to the Jews, whom he continually blessed, but who did not do things that please him]: “A man planted a fig tree on his farmland. ([Each year/Many times]) he came to it looking for figs, but there were no figs.
7 Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
Then he said to the gardener, ‘Look [here]! I have been looking for fruit on this fig tree every year for the past three years, but there have been no figs. Cut it down! (It is just using up the nutrients in the soil for nothing!/Why should it continue using up the [nutrients in] the soil [for nothing]?) [RHQ]’
8 Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
But the gardener replied to the owner, ‘Sir, leave it here for another year. I will dig around it and put manure around it.
9 In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
If it bears fruit next year, we [(inc)] will allow it to keep growing. If it does not bear fruit next year, you [(sg)] can cut it down.’”
10 Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
One (Sabbath/Jewish day of rest), [Jesus] was teaching people in one of the Jewish meeting places.
11 Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
There was a woman there whom an evil spirit [MTY] had crippled for 18 years. She was always bent over; she could not stand up straight.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
When Jesus saw her, he called her over to him. He said to her, “Woman, [I am] freeing you [(sg)] from your illness!”
13 Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
He put his hands on her. Immediately she stood up straight, and she praised God!
14 Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
But the man in charge (of the synagogue/of the meeting place) was angry because Jesus had healed her (on the Sabbath/on the Jewish rest day). [He considered that healing was doing work]. So he said to the people, “There are six days [each week] in which [our Jewish] laws permit people to work. [If you need healing], those are the days to come ([to the synagogue/to the meeting place]) and be healed. Do not come on our Jewish day of rest!”
15 Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
Then the Lord replied to him, “You [(sg) and your fellow religious leaders are] hypocrites! (On the Sabbath/On our Jewish day of rest), [just like on every other day], (each of you unties his ox or donkey, and then leads it from the food trough to where it can drink water./does not each of you untie his ox or donkey, and then lead it from the food trough to where it can drink water?) [RHQ] [That is work, too]!
16 Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
This woman [is more important than an animal; she is a Jew], descended from Abraham! But Satan has [kept her] [MET] [crippled] for 18 years, [as though] he had tied her up [and not let her escape]! So (it is certainly right that she be freed {that [I] free her}, [even if this] is a Sabbath day!/was it not right that she be freed {that [I] free her}, [even if this] is a Jewish rest day?) [RHQ]”
17 Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
After Jesus said that, all the people [there] who opposed him were ashamed. But all the [other] people [there] were happy about all the wonderful things he was doing.
18 Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
Then Jesus said, “(I will tell you how [the number of people who let] God rule [MET] [their lives will increase]./Do you know how [the number of people who let] God rule [MET] [their lives will increase]?) [RHQ] I will tell you what I can compare it to.
19 Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
It is like a [tiny] mustard seed that a man planted in his field. It grew until it became [big, like] a tree. It was [so big that] birds built nests in its branches.”
20 Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
Then he said, “I will tell [RHQ] you something else, to illustrate how the people who let God rule [MET] [their lives can influence their society more and more].
21 Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
It is like [a little bit of] yeast that a woman mixed with about 50 pounds of flour. [That small amount of yeast made] the whole batch of dough swell up.”
22 Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
[Jesus] continued traveling, along [with his disciples], through various towns and villages on the way to Jerusalem. As they went, he was teaching [the people].
23 Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
Someone asked him, “Lord, will there be only a few people who are saved {whom [God] saves}?” He replied to them, “[There will not be many, because] the way [to heaven] [MET] is [like] a narrow door.
24 “Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
[Therefore, try hard] to enter that narrow doorway, because I tell you that many people will try to enter [heaven by some other way], but they will not be able to get in.
25 In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
[God is like] the owner of a house. [Some day] he will lock his door. Then [some of] you will begin to stand outside that door and knock. You will say, ‘Lord, open the door for us!’ But he will reply, ‘[No, I will not open it, because] I do not know you, and I do not know where you are from!’
26 Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
Then you will say, ‘([You must have forgotten!/Surely you know us, because]) [RHQ] we [(exc)] ate [meals] with you [(sg)], and you taught [people] in the streets of our [towns]’!
27 Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
But he will say, ‘[I tell you again], I do not know you, and I do not know where you are from. You [are] wicked people! Get away from here!’”
28 Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
Then Jesus continued, saying, “[From where God will send you], you will see Abraham and Isaac and Jacob in the distance. All the prophets [who lived long ago will also be there], in the kingdom where God [is ruling]. But you will be outside, crying and grinding your teeth [because you will have severe pain]!
29 Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
Furthermore, many [non-Jewish] people will [be inside]. There will be ones who have come from [lands to] the north, east, south, and west. They will be feasting in (that place where God is ruling/God’s kingdom).
30 Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
Think about this: Some people whom others do not [consider] important [now, God will make] them very important [then], and some people whom [others consider] very important [now, God will make] to be not important [then].”
31 Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
At that very time, some Pharisees came and said to Jesus, “Leave this area, because [the ruler] Herod [Antipas] wants to kill you [(sg)]!”
32 Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
He replied to them, “Herod is [MET] [as cruel as] a fox, [but also as insignificant as a fox]. [So I do not worry about him]. But [to show him that no one can harm me until it is the time and place God has determined], go tell him this [message from me]: ‘Listen! I am expelling demons and performing miracles today, and [I will continue doing] it for a short time. After that, I will finish my work.
33 Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
But I must continue my trip [to Jerusalem] during the coming days, because [they killed many other] prophets there, and [since I am also a prophet], no other place is appropriate for people to kill [me].’”
34 Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
[Then Jesus said], “O [people of] [MTY] Jerusalem [APO]! You killed the prophets [who lived long ago, and you killed others], whom [God] sent to you, [by throwing] stones [at them]. Many times I wanted to gather you together [to protect you] [SIM] like a hen gathers her young chicks under her wings. But you did not want [me to do that].
35 Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”
So listen to this: Your city [MTY] (OR, your temple) is going to be abandoned (OR, God will no longer protect it). I will [MTY] also tell you this: I [will enter your city only once more. After that], you will not see me until the time when [I return and] you say [about me], ‘God is truly pleased with this man who comes with God’s authority [MTY]!’”