< Luka 13 >

1 A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
Men på den samme Tid var der nogle til Stede, som fortalte ham om de Galilæere, hvis Blod Pilatus havde blandet med deres Ofre.
2 Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
Og han svarede og sagde til dem: "Mene I, at disse Galilæere vare Syndere frem for alle Galilæere, fordi de have lidt dette?
3 A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
Nej, siger jeg eder; men dersom I ikke omvende eder, skulle I alle omkomme ligeså.
4 Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Eller hine atten, som Tårnet i Siloam faldt ned over og ihjelslog, mene I, at de vare skyldige fremfor alle Mennesker, som bo i Jerusalem?
5 Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
Nej, siger jeg eder; men dersom I ikke omvende eder, skulle I alle omkomme ligeså."
6 Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
Men han sagde denne Lignelse: "En havde et Figentræ, som var plantet i hans Vingård; og han kom og ledte efter Frugt derpå og fandt ingen.
7 Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
Men han sagde til Vingårdsmanden: Se, i tre År er jeg nu kommen og har ledt efter Frugt på dette Figentræ og ingen fundet; hug det om; hvorfor skal det tilmed gøre Jorden unyttig?
8 Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
Men han svarede og sagde til ham: Herre! lad det stå endnu dette År, indtil jeg får gravet om det og gødet det;
9 In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
måske vil det bære Frugt i Fremtiden; men hvis ikke, da hug det om!"
10 Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
Men han lærte i en af Synagogerne på Sabbaten.
11 Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
Og se, der var en Kvinde, som havde haft en Svagheds Ånd i atten År, og hun var sammenbøjet og kunde aldeles ikke rette sig op.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
Men da Jesus så hende, kaldte han på hende og sagde til hende: "Kvinde! du er løst fra din Svaghed."
13 Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
Og han lagde Hænderne på hende; og straks rettede hun sig op og priste Gud.
14 Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
Men Synagogeforstanderen, som var vred, fordi Jesus helbredte på Sabbaten, tog til Orde og sagde til Folkeskaren: "Der er seks Dage, på hvilke man bør arbejde; kommer derfor på dem og lader eder helbrede, og ikke på Sabbatsdagen!"
15 Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
Men Herren svarede ham og sagde: "I Hyklere! løser ikke enhver iblandt eder sin Okse eller sit Asen fra Krybben på Sabbaten og fører dem til Vands?
16 Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
Men denne, som er en Abrahams Datter, hvem Satan har bundet, se, i atten År, burde hun ikke løses fra dette Bånd på Sabbatsdagen?"
17 Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
Og da han sagde dette, bleve alle hans Modstandere beskæmmede; og hele Skaren glædede sig over alle de herlige Gerninger, som gjordes af ham.
18 Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
Han sagde da: "Hvad ligner Guds Rige, og hvormed skal jeg ligne det?
19 Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
Det ligner et Sennepskorn, som et Menneske tog og lagde i sin Have; og det voksede og blev til et Træ, og Himmelens Fugle byggede Rede i dets Grene."
20 Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
Og atter sagde han: "Hvormed skal jeg ligne Guds Rige?
21 Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
Det ligner en Surdejg, som en Kvinde tog og lagde ned i tre Mål Mel, indtil det blev syret alt sammen."
22 Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
Og han gik igennem Byer og Landsbyer og lærte og tog Vejen til Jerusalem.
23 Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
Men en sagde til ham: "Herre mon de ere få, som blive frelste?" Da sagde han til dem:
24 “Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
"Kæmper for at komme ind igennem den snævre Port; thi mange, siger jeg eder, skulle søge at komme ind og ikke formå det.
25 In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
Fra den Stund Husbonden er stået op og har lukket Døren, og I begynde at stå udenfor og banke på Døren og sige: Herre, luk op for os! da vil han svare og sige til eder: Jeg kender eder ikke, hvorfra I ere;
26 Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
da skulle I begynde at sige: vi spiste og drak for dine Øjne, og du lærte på vore Gader,
27 Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
og han skal sige: Jeg siger eder, jeg kender eder ikke, hvorfra I ere; viger bort fra mig, alle I, som øve Uret!
28 Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
Der skal der være Gråd og Tænders Gnidsel, når I må se Abraham og Isak og Jakob og alle Profeterne i Guds Rige, men eder selv blive kastede udenfor.
29 Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
Og de skulle komme fra Øster og Vester og fra Norden og Sønden og sidde til Bords i Guds Rige.
30 Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
Og se, der er sidste, som skulle være iblandt de første, og der er første, som skulle være iblandt de sidste."
31 Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
I den samme Stund kom nogle Farisæere og sagde til ham: "Gå bort, og drag herfra; thi Herodes vil slå dig ihjel."
32 Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
Og han sagde til dem: "Går hen og siger til denne Ræv: Se, jeg uddriver onde Ånder og fuldfører Helbredelser i Dag og i Morgen, og på den tredje dag fuldendes jeg.
33 Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
Dog bør jeg vandre i Dag og i Morgen og den Dag derefter; thi det sømmer sig ikke, at en Profet dræbes uden for Jerusalem.
34 Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
Jerusalem! Jerusalem! som ihjelslår Profeterne og stener dem, som ere sendte til dig! hvor ofte vilde jeg samle dine Børn, ligesom en Høne samler sine Kyllinger under Vingerne! Og I vilde ikke.
35 Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”
Se, eders Hus overlades til eder selv. Men jeg siger eder: I skulle ingenlunde se mig, førend den Tid kommer, da I sige: Velsigtnet være den, som kommer, i Herrens Navn!"

< Luka 13 >