< Luka 12 >

1 Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. “Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.
Meanwhile, when a crowd of many thousands had gathered together, so much so that they trampled on each other, he began to tell his disciples first of all, "Beware of the yeast of the Pharisees, which is hypocrisy.
2 Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba.
But there is nothing covered up, that will not be revealed, nor hidden, that will not be known.
3 Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.
Therefore whatever you have said in the darkness will be heard in the light. What you have spoken in the ear in the inner chambers will be proclaimed on the housetops.
4 Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi.
"I tell you, my friends, do not be afraid of those who kill the body, and after that have no more that they can do.
5 Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
But I will warn you whom you should fear. Fear him, who after he has killed, has power to cast into Gihana. Yes, I tell you, fear him. (Geenna g1067)
6 Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba.
"Are not five sparrows sold for two assaria coins? Not one of them is forgotten by God.
7 Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.
But the very hairs of your head are all numbered. Therefore do not be afraid. You are of more value than many sparrows.
8 Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah.
"I tell you, everyone who confesses me before people, him will the Son of Man also confess before the angels of God;
9 Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah.
but the one who denies me in the presence of people will be denied in the presence of the angels of God.
10 Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Everyone who speaks a word against the Son of Man will be forgiven, but those who blaspheme against the Rukha d'Qudsha will not be forgiven.
11 Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce.
When they bring you before the synagogues, the rulers, and the authorities, do not be anxious how or what you will answer, or what you will say;
12 Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci.”
for the Rukha d'Qudsha will teach you in that same hour what you must say."
13 Sai wani a cikin taron ya ce masa, “Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni
And someone in the crowd said to him, "Teacher, tell my brother to divide the inheritance with me."
14 Yesu ya ce masa, “Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?”
But he said to him, "Man, who made me a judge or an arbitrator over you?"
15 Sai kuma ya ce masu, “Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba.”
He said to them, "Beware. Keep yourselves from all covetousness, for a man's life does not consist of the abundance of the things which he possesses."
16 Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, “Gonar wani mutum ta bada amfani sosai,
He spoke a parable to them, saying, "The ground of a certain rich man brought forth abundantly.
17 ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?'
He reasoned within himself, saying, 'What will I do, because I do not have room to store my crops?'
18 Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa.
He said, 'This is what I will do. I will pull down my barns, and build bigger ones, and there I will store all my grain and my goods.
19 Sai in ce da raina, “Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna.”
I will tell my soul, "Soul, you have many goods laid up for many years. Take your ease, eat, drink, be merry."'
20 Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?'
"But God said to him, 'You foolish one, tonight your soul is required of you. The things which you have prepared—whose will they be?'
21 Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah.”
So is he who lays up treasure for himself, and is not rich toward God."
22 Yesu, ya ce da almajiransa, “Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku.
He said to his disciples, "Therefore I tell you, do not be anxious for your life, what you will eat, nor yet for your body, what you will wear.
23 Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Life is more than food, and the body is more than clothing.
24 Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja!
Consider the ravens: they do not sow, they do not reap, they have no warehouse or barn, and God feeds them. How much more valuable are you than birds.
25 Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki?
Which of you by being anxious can add a cubit to his height?
26 Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?
If then you are not able to do even the least things, why are you anxious about the rest?
27 Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba.
Consider the lilies, how they grow. They do not toil, neither do they spin; yet I tell you, even Shelemun in all his glory was not arrayed like one of these.
28 Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!
But if this is how God clothes the grass in the field, which today exists, and tomorrow is cast into the oven, how much more will he clothe you, O you of little faith?
29 Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini.
Do not seek what you will eat or what you will drink; neither be anxious.
30 Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.
For the nations of the world seek after all of these things, but your Father knows that you need these things.
31 Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su.
But seek his Kingdom, and these things will be added to you.
32 Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.
Do not be afraid, little flock, for it is your Father's good pleasure to give you the Kingdom.
33 Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba.
Sell that which you have, and give gifts to the needy. Make for yourselves purses which do not grow old, a treasure in the heavens that does not fail, where no thief approaches, neither moth destroys.
34 Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.
For where your treasure is, there will your heart be also.
35 Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe,
"Let your waist be girded and your lamps burning.
36 ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.
Be like people watching for their lord, when he returns from the marriage feast; that, when he comes and knocks, they may immediately open to him.
37 Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa.
Blessed are those servants, whom the lord will find watching when he comes. Truly I tell you, that he will dress himself, and make them recline, and will come and serve them.
38 Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.
And if he comes in the second watch, or even in the third, and finds them so, blessed are they.
39 Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba.
But know this, that if the master of the house had known in what hour the thief was coming, he would have watched and not have allowed his house to be broken into.
40 Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba.”
Therefore be ready also, for the Son of Man is coming in an hour that you do not expect him."
41 Sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?”
And Kipha said, "Lord, are you telling this parable to us, or to everyone?"
42 Sai Ubangiji ya ce, “Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci?
The Lord said, "Who then is the faithful and wise steward, whom his lord will set over his household, to give them their portion of food at the right time?
43 Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi.
Blessed is that servant whom his lord will find doing so when he comes.
44 Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.
Truly I tell you, that he will set him over all that he has.
45 Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu,
But if that servant says in his heart, 'My lord delays his coming,' and begins to beat the menservants and the maidservants, and to eat and drink, and to be drunk,
46 ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.
then the lord of that servant will come in a day when he is not expecting him, and in an hour that he does not know, and will cut him in two, and place his portion with the unfaithful.
47 Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa.
That servant, who knew his lord's will, and did not prepare, nor do what he wanted, will be beaten with many stripes,
48 Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.
but he who did not know, and did things worthy of stripes, will be beaten with few stripes. To whomever much is given, of him will much be required; and to whom much was entrusted, of him more will be asked.
49 Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama.
"I came to throw fire on the earth. I wish it were already kindled.
50 Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!
But I have a baptism to be baptized with, and how distressed I am until it is accomplished.
51 Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa.
Do you think that I have come to give peace in the earth? I tell you, no, but rather division.
52 Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun.
For from now on, there will be five in one house divided, three against two, and two against three.
53 Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta.”
They will be divided, father against son, and son against father; mother against daughter, and daughter against her mother; mother-in-law against her daughter-in-law, and daughter-in-law against her mother-in-law."
54 Yesu, ya kuma gaya wa taron, “Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama.
He said to the crowds also, "When you see a cloud rising from the west, immediately you say, 'A shower is coming,' and so it happens.
55 Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru.
When a south wind blows, you say, 'There will be a scorching heat,' and it happens.
56 Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?
Hypocrites. You know how to interpret the appearance of the earth and the sky, but why do you not know how to interpret this time?
57 Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku?
Why do you not judge for yourselves what is right?
58 Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba.
For when you are going with your adversary before the magistrate, try diligently on the way to be released from him, lest perhaps he drag you to the judge, and the judge deliver you to the officer, and the officer throw you into prison.
59 Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?
I tell you, you will by no means get out of there, until you have paid the very last penny."

< Luka 12 >