< Luka 12 >
1 Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. “Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.
Da imidlertid mange Tusinde Mennesker havde samlet sig, saa at de traadte paa hverandre, begyndte han at sige til sine Disciple: „Tager eder først og fremmest i Vare for Farisæernes Surdejg, som er Hykleri.
2 Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba.
Men intet er skjult, som jo skal aabenbares, og intet er lønligt, som jo skal blive kendt.
3 Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.
Derfor, alt hvad I have sagt i Mørket, skal høres i Lyset; og hvad I have talt i Øret i Kamrene, skal blive prædiket paa Tagene.
4 Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi.
Men jeg siger til eder, mine Venner! frygter ikke for dem, som slaa Legemet ihjel og derefter ikke formaa at gøre mere.
5 Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa. (Geenna )
Men jeg vil vise eder, for hvem I skulle frygte: Frygter for ham, som har Magt til, efter at have slaaet ihjel, at kaste i Helvede; ja, jeg siger eder: Frygter for ham! (Geenna )
6 Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba.
Sælges ikke fem Spurve for to Penninge? og ikke een af dem er glemt hos Gud.
7 Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.
Ja, endog Haarene paa eders Hoved ere alle talte; frygter ikke, I ere mere værd end mange Spurve.
8 Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah.
Men jeg siger eder: Enhver, som vedkender sig mig for Menneskene, ham vil ogsaa Menneskesønnen vedkende sig for Guds Engle.
9 Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah.
Og den, som har fornægtet mig for Menneskene, skal fornægtes for Guds Engle.
10 Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Og enhver, som taler et Ord imod Menneskesønnen, ham skal det forlades; men den, som har talt bespotteligt imod den Helligaand, ham skal det ikke forlades.
11 Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce.
Men naar de føre eder frem for Synagogerne og Øvrighederne og Myndighederne, da bekymrer eder ikke for, hvorledes eller hvormed I skulle forsvare eder, eller hvad I skulle sige.
12 Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci.”
Thi den Helligaand skal lære eder i den samme Time, hvad I bør sige.”
13 Sai wani a cikin taron ya ce masa, “Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni
Men en af Skaren sagde til ham: „Mester! sig til min Broder, at han skal dele Arven med mig.”
14 Yesu ya ce masa, “Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?”
Men han sagde til ham: „Menneske! hvem har sat mig til Dommer eller Deler over eder?”
15 Sai kuma ya ce masu, “Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba.”
Og han sagde til dem: „Ser til og vogter eder for al Havesyge; thi ingens Liv beror paa, hvad han ejer, selv om han har Overflod.”
16 Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, “Gonar wani mutum ta bada amfani sosai,
Og han sagde en Lignelse til dem: „Der var en rig Mand, hvis Mark havde baaret godt.
17 ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?'
Og han tænkte ved sig selv og sagde: Hvad skal jeg gøre? thi jeg har ikke Rum, hvori jeg kan samle min Afgrøde.
18 Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa.
Og han sagde: Dette vil jeg gøre, jeg vil nedbryde mine Lader og bygge dem større, og jeg vil samle deri al min Afgrøde og mit Gods;
19 Sai in ce da raina, “Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna.”
og jeg vil sige til min Sjæl: Sjæl! du har mange gode Ting liggende for mange Aar; slaa dig til Ro, spis, drik, vær lystig!
20 Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?'
Men Gud sagde til ham: Du Daare! i denne Nat kræves din Sjæl af dig; men hvem skal det høre til, som du har beredt?
21 Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah.”
Saaledes er det med den, som samler sig Skatte og ikke er rig i Gud.”
22 Yesu, ya ce da almajiransa, “Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku.
Men han sagde til sine Disciple: „Derfor siger jeg eder: Bekymrer eder ikke for Livet, hvad I skulle spise; ikke heller for Legemet, hvad I skulle iføre eder.
23 Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Livet er mere end Maden, og Legemet mere end Klæderne.
24 Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja!
Giver Agt paa Ravnene, at de hverken saa eller høste, og de have ikke Forraadskammer eller Lade, og Gud føder dem; hvor langt mere værd end Fuglene ere dog I?
25 Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki?
Og hvem af eder kan ved at bekymre sig lægge en Alen til sin Vækst?
26 Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?
Formaa I altsaa ikke engang det mindste, hvorfor bekymre I eder da for det øvrige?
27 Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba.
Giver Agt paa Lillierne, hvorledes de vokse; de arbejde ikke og spinde ikke; men jeg siger eder: End ikke Salomon i al sin Herlighed var klædt som en af dem.
28 Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!
Klæder da Gud saaledes det Græs paa Marken, som i Dag staar og i Morgen kastes i Ovnen, hvor meget mere eder, I lidettroende!
29 Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini.
Og I, spørger ikke efter, hvad I skulle spise, og hvad I skulle drikke; og værer ikke ængstelige!
30 Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.
Thi efter alt dette søge Hedningerne i Verden; men eders Fader ved, at I have disse Ting nødig.
31 Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su.
Men søger hans Rige, saa skulle disse Ting gives eder i Tilgift.
32 Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.
Frygt ikke, du lille Hjord! thi det var eders Fader velbehageligt at give eder Riget.
33 Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba.
Sælger, hvad I eje, og giver Almisse! Gører eder Punge, som ikke ældes, en Skat i Himlene, som ikke slipper op, der hvor ingen Tyv kommer nær, og intet Møl ødelægger.
34 Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.
Thi hvor eders Skat er, der vil ogsaa eders Hjerte være.
35 Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe,
Eders Lænder være omgjordede, og eders Lys brændende!
36 ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.
Og værer I ligesom Mennesker, der vente paa deres Herre, naar han vil bryde op fra Brylluppet, for at de straks, naar han kommer og banker paa, kunne lukke op for ham.
37 Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa.
Salige ere de Tjenere, som Herren finder vaagne, naar han kommer. Sandelig, siger jeg eder, at han skal binde op om sig og sætte dem til Bords og gaa om og varte dem op.
38 Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.
Og dersom han kommer i den anden Nattevagt og kommer i den tredje Nattevagt og finder det saaledes, da ere disse Tjenere salige.
39 Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba.
Men dette skulle I vide, at dersom Husbonden vidste, i hvilken Time Tyven vilde komme, da vaagede han og tillod ikke, at der skete Indbrud i hans Hus.
40 Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba.”
Vorder ogsaa I rede; thi Menneskesønnen kommer i den Time, som I ikke mene.”
41 Sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?”
Men Peter sagde til ham: „Herre! siger du denne Lignelse til os eller ogsaa til alle?”
42 Sai Ubangiji ya ce, “Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci?
Og Herren sagde: „Hvem er vel den tro og forstandige Husholder, som Herren vil sætte over sit Tyende til at give dem den bestemte Kost i rette Tid?
43 Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi.
Salig er den Tjener, hvem hans Herre, naar han kommer, finder handlende saaledes.
44 Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.
Sandelig, siger jeg eder, han skal sætte ham over alt, hvad han ejer.
45 Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu,
Men dersom hin Tjener siger i sit Hjerte: „Min Herre tøver med at komme” og saa begynder at slaa Karlene og Pigerne og at spise og drikke og beruse sig,
46 ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.
da skal den Tjeners Herre komme paa den Dag, han ikke venter, og i den Time, han ikke ved, og hugge ham sønder og give ham hans Lod sammen med de utro.
47 Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa.
Men den Tjener, som har kendt sin Herres Villie og ikke har truffet Forberedelser eller handlet efter hans Villie, skal have mange Hug;
48 Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.
men den, som ikke har kendt den og har gjort, hvad der er Hug værd, skal have faa Hug. Enhver, hvem meget er givet, af ham skal man kræve meget; og hvem meget er betroet, af ham skal man forlange mere.
49 Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama.
Ild er jeg kommen at kaste paa Jorden, og hvor vilde jeg, at den var optændt allerede!
50 Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!
Men en Daab har jeg at døbes med, og hvor ængstes jeg, indtil den er fuldbyrdet!
51 Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa.
Mene I, at jeg er kommen for at give Fred paa Jorden? Nej, siger jeg eder, men Splid.
52 Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun.
Thi fra nu af skulle fem i eet Hus være i Splid indbyrdes, tre imod to, og to imod tre.
53 Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta.”
De skulle være i Splid, Fader med Søn og Søn med Fader, Moder med Datter og Datter med Moder, Svigermoder med sin Svigerdatter og Svigerdatter med sin Svigermoder.”
54 Yesu, ya kuma gaya wa taron, “Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama.
Men han sagde ogsaa til Skarerne: „Naar I se en Sky komme op i Vester, sige I straks: Der kommer Regn, og det sker saaledes.
55 Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru.
Og naar I se en Søndenvind blæse, sige I: Der kommer Hede; og det sker.
56 Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?
I Hyklere! Jordens og Himmelens Udseende vide I at skønne om; men hvorfor have I da intet Skøn om den nærværende Tid?
57 Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku?
Og hvorfor dømme I ikke ogsaa fra eder selv, hvad der er det rette?
58 Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba.
Thi medens du gaar hen med din Modpart til Øvrigheden, da gør dig Flid paa Vejen for at blive forligt med ham, for at han ikke skal trække dig for Dommeren, og Dommeren skal overgive dig til Slutteren, og Slutteren skal kaste dig i Fængsel.
59 Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?
Jeg siger dig: Du skal ingenlunde komme ud derfra, førend du faar betalt endog den sidste Skærv.”