< Luka 11 >
1 Wani lokaci, Yesu yana yin addu'a a wani wuri, sai daya daga cikin almajiransa yace da shi, “Ubangiji, ka koya mana yin addu'a kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa.”
Og det skete, da han var paa et Sted og bad, at en af hans Disciple sagde til ham, da han holdt op: „Herre! lær os at bede, som ogsaa Johannes lærte sine Disciple.”
2 Yesu ya ce ma su, “Sa'anda ku ke yin addu'a ku ce, 'Uba a tsarkake sunanka. Mulkin ka ya zo.
Da sagde han til dem: „Naar I bede, da siger: Fader, helliget vorde dit Navn; komme dit Rige;
3 Ka ba mu abin da za mu ci a kowacce rana.
giv os hver Dag vort daglige Brød;
4 Gafarta mana zunubanmu, kamar yadda muke gafarta ma wadanda suke mana laifi. Kada ka kai mu cikin jaraba.'”
og forlad os vore Synder, thi ogsaa vi forlade hver, som er os skyldig; og led os ikke i Fristelse!”
5 Yesu ya ce masu, “Wanene a cikinku idan yana da aboki, za ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, ''Aboki, ka ba ni rancen dunkulen gurasa guda uku,
Og han sagde til dem: „Om nogen af eder har en Ven og gaar til ham ved Midnat og siger til ham: Kære! laan mig tre Brød,
6 da ya ke wani abokina ya iso yanzu daga tafiya, kuma ba ni da abin da zan ba shi ya ci,'
efterdi en Ven af mig er kommen til mig fra Rejsen, og jeg har intet at sætte for ham;
7 Sai wanda yake ciki, ya amsa, ya ce, 'Kada ka dame ni. Na riga na rufe kofa ta, kuma ni da yarana mun riga mun kwanta. Ba zan iya tashi in ba ka gurasa ba.'
og hin saa svarer derinde fra og siger: Vold mig ikke Besvær; Døren er allerede lukket, og mine Børn ere med mig i Seng; jeg kan ikke staa op og give dig det:
8 Na fada maku, ko da bai tashi ya ba ka gurasar ba, a matsayin abokinsa, ba ka ji kunya ba, ka nace da rokonsa, za ya tashi ya ba ka dukan yawan gurasar da kake bukata.
da, siger jeg eder, om han end ikke staar op og giver ham det, fordi han er hans Ven, saa staar han dog op for hans Paatrængenheds Skyld og giver ham alt, hvad han trænger til.
9 Ni kuma ina ce maku, ku roka za a ba ku; ku nema za ku samu; ku kwankwasa za a bude maku.
Og jeg siger eder: Beder, saa skal eder gives; søger, saa skulle I finde; banker paa, saa skal der lukkes op for eder.
10 Domin dukan wanda yake roko ya na karba; dukan wanda ya ke nema kuma yana samu; kuma wanda yake kwankwasawa, za a bude masa.
Thi hver den, som beder, han faar, og den, som søger, han finder, og den, som banker paa, for ham skal der lukkes op.
11 Wanne uba ne a cikinku, idan dansa ya tambaye shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon kifi?
Men hvilken Fader iblandt eder vil give sin Søn en Sten, naar han beder om Brød, eller naar han beder om en Fisk, mon han da i Stedet for en Fisk vil give ham en Slange?
12 Ko kuwa idan ya tambaye shi kwai, za ya ba shi kunama?
Eller naar han beder om et Æg, mon han da vil give ham en Skorpion?
13 To, da yake ku da kuke masu mugunta kun san ku ba 'yanyan ku abu mai kyau. Yaya fa ga Ubanku wanda yake cikin sama, za ya ba da Ruhu Mai Tsarki ga wadanda suka roke shi?”
Dersom da I, som ere onde, vide at give eders Børn gode Gaver, hvor meget mere skal da Faderen fra Himmelen give den Helligaand til dem, som bede ham!”
14 Wani lokaci, Yesu yana fitar da wani beben aljani. Sa'adda aljanin ya fita, sai mutumin da yake bebe ya yi magana. Sai taron mutanen suka yi mamaki!
Og han uddrev en ond Aand, og den var stum; men det skete, da den onde Aand var udfaren, talte den stumme, og Skarerne forundrede sig.
15 Amma, wadansu daga cikin mutanen suka ce, “Da ikon Ba'alzabuba sarkin aljanu ne yake fitar da aljanu.”
Men nogle af dem sagde: „Ved Beelzebul, de onde Aanders Fyrste, uddriver han de onde Aander.”
16 Wadansu suka gwada shi, suka nemi ya nuna masu wata alama daga sama.
Men andre fristede ham og forlangte af ham et Tegn fra Himmelen.
17 Amma Yesu da yake ya san tunaninsu, ya ce da su, “Dukan mulkin da ya rabu biyu, gaba da kansa, ya rushe kenan, kuma idan gida ya rabu biyu, gaba da kansa za ya fadi.
Men da han kendte deres Tanker, sagde han til dem: „Hvert Rige, som er kommet i Splid med sig selv, lægges øde, og Hus falder over Hus.
18 Idan Shaidan ya rabu biyu gaba da kansa, ta yaya mulkinsa zai iya tsayawa? Gama kun ce ina fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba.
Men hvis ogsaa Satan er kommen i Splid med sig selv, hvorledes skal hans Rige da bestaa? Thi I sige, at jeg uddriver de onde Aander ved Beelzebul.
19 Idan ni na fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba, ta wurin wa wadanda suke bin ku suke fitar da aljanu? Saboda haka, su ne zasu zama masu yi maku shari'a.
Men dersom jeg uddriver de onde Aander ved Beelzebul, ved hvem uddrive da eders Sønner dem? Derfor skulle de være eders Dommere.
20 Amma idan daga wurin Allah na ke fitar da aljanu, to, ya zama ke nan mulkin Allah ya zo wurinku.
Men dersom jeg uddriver de onde Aander ved Guds Finger, da er jo Guds Rige kommet til eder.
21 Idan mutum mai karfi, mai kayan fada ya tsare gidansa, kayansa za su tsira.
Naar den stærke bevæbnet vogter sin Gaard, bliver det, han ejer, i Fred.
22 Amma idan wani mutum wanda ya fi shi karfi ya zo ya ci nasara a kansa, zai dauke kayan fadan daga wurin mutumin, kuma ya kwashe kayansa.
Men naar en stærkere end han er kommen over ham og har overvundet ham, da tager han hans fulde Rustning, som han forlod sig paa, og uddeler hans Bytte.
23 Wanda ba ya tare da ni, gaba da ni ya ke yi, kuma wanda ba ya tattarawa tare da ni, watsarwa yake yi.
Den, som ikke er med mig, er imod mig; og den, som ikke samler med mig, adspreder.
24 Idan kazamin ruhu ya fita daga cikin mutum, ya kan bi ta wurin busassun wurare yana neman wurin da zai huta. Idan bai samu ba sai ya ce, 'Bari in koma gidana inda na baro.
Naar den urene Aand er faren ud af Mennesket, vandrer den igennem vandløse Steder og søger Hvile; og naar den ikke finder den, siger den: Jeg vil vende tilbage til mit Hus, som jeg gik ud af.
25 Sa'adda ya dawo, ya tarar an share gidan, an kuma gyara shi tsaf.
Og naar den kommer, finder den det fejet og prydet.
26 Sai ya je ya dauko wadansu aljanu guda bakwai wadanda su ka fi shi mugunta, su zo su zauna a wurin. Sai karshen mutumin nan ya fi farkonsa muni.”
Da gaar den bort og tager syv andre Aander med sig, som ere værre end den selv, og naar de ere komne derind, bo de der; og det sidste bliver værre med dette Menneske end det første.”
27 Ya zama, lokacin da ya ke fadin wadannan abubuwa, wata mace ta tada muryarta a cikin taron mutanen ta ce da shi, “Mai albarka ne cikin da ya haife ka, da maman da ka sha.”
Men det skete, medens han sagde disse Ting, da opløftede en Kvinde af Skaren sin Røst og sagde til ham: „Saligt er det Liv, som bar dig, og de Bryster, som du diede.”
28 Sai shi kuma ya ce, “Masu albarka ne wadanda suke jin maganar Allah suke yin biyayya da ita.”
Men han sagde: „Ja, salige ere de, som høre Guds Ord og bevare det.”
29 Lokacin da mutane suke kara taruwa, sai ya fara cewa, “Wannan tsara, muguwar tsara ce. Ta na neman alama, Ko da yake ba wata alamar da za a bata sai irin ta Yunusa.
Men da Skarerne strømmede til, begyndte han at sige: „Denne Slægt er en ond Slægt; et Tegn forlanger den, og der skal intet Tegn gives den uden Jonas's Tegn.
30 Domin kamar yadda Yunusa ya zama alama ga mutanen Neneba, haka kuma Dan Mutum za ya zama alama ga wannan tsara.
Thi ligesom Jonas blev et Tegn for Niniviterne, saaledes skal ogsaa Menneskesønnen være det for denne Slægt.
31 Sarauniyar Kudu, za ta tsaya ta yi shari'a da mutanen wannan tsara, kuma za ta kashe su, gama ta zo daga wuri mai nisa domin ta saurari hikimar Sulaimanu. Kuma ga wani wanda ya fi Sulaimanu a nan.
Sydens Dronning skal oprejses ved Dommen sammen med Mændene af denne Slægt og fordømme dem; thi hun kom fra Jordens Grænser for at høre Salomons Visdom; og se, her er mere end Salomon.
32 Mutanen Neneba, za su tsaya shari'a da matanen wannan tsara, kuma za su kashe su. Gama sun ji wa'azin Yunusa sun tuba. Kuma ga wani wanda ya fi Yunusa a nan.
Mænd fra Ninive skulle opstaa ved Dommen sammen med denne Slægt og fordømme den; thi de omvendte sig ved Jonas's Prædiken; og se, her er mere end Jonas.
33 Ba wanda zai kunna fitila ya boye ta, ko kuwa ya sa ta a karkashin kasko, amma zai sa ta a mazaunin ta domin dukan wanda ya shiga dakin ya ga haske.
Ingen tænder et Lys og sætter det i Skjul, ikke heller under Skæppen, men paa Lysestagen, for at de, som komme ind, kunne se dets Skin.
34 Idon ku shine fitilar jikinku. Idan idonku yana gani sosai, jikinku zai cika da haske. Amma idan idonku ba ya gani sosai, jikinku zai cika da duhu.
Dit Øje er Legemets Lys; naar dit Øje er sundt, er ogsaa hele dit Legeme lyst, men dersom det er daarligt, er ogsaa dit Legeme mørkt.
35 Ku yi hankali fa, domin kada hasken da ya ke wurinku ya zama duhu.
Se derfor til, at det Lys, der er i dig, ikke er Mørke.
36 Idan dukan jikinku yana cike da haske, babu duhu ko kadan, to sai dukan jikinku ya zama kamar fitilar da take bada haskenta a bisanku.”
Dersom da hele dit Legeme er lyst, saa at ingen Del deraf er mørk, vil det være helt lyst, som naar Lyset bestraaler dig med sin Glans.”
37 Sa'adda ya gama jawabi, sai wani Bafarise ya ce da shi ya zo gidansa ya ci abinci, sai Yesu ya shiga ya zauna.
Men idet han talte, beder en Farisæer ham om, at han vilde spise Middagsmaaltid hos ham, og han gik ind og satte sig til Bords.
38 Sai Bafarisen ya yi mamaki da ganin bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba.
Men Farisæeren forundrede sig, da han saa, at han ikke toede sig først før Maaltidet.
39 Amma sai Ubangiji ya ce da shi, “Ku Farisawa kuna tsabtace bayan kofi da bangaji, amma cikin yana cike da kazamta da mugunta.
Men Herren sagde til ham: „I Farisæere rense nu det udvendige af Bægeret og Fadet; men eders Indre er fuldt af Rov og Ondskab.
40 Ku mutane marasa tunani, wanda ya yi wajen, ba shine ya yi cikin ba?
I Daarer! han, som gjorde det ydre, gjorde han ikke ogsaa det indre?
41 Ku bayar da abin da ke ciki ga matalauta, kuma dukan abu zai zamar maku da tsafta.
Men giver det, som er indeni, til Almisse; se, saa ere alle Ting eder rene.
42 Amma kaitonku Farisawa, gama kuna karbar zakka da daddoya da karkashi da kowanne irin ganye na lambu, amma kun watsar da adalci da kaunar Allah. Dole ne a yi adalci, a kaunaci Allah, a yi sauran abubuwan kuma.
Men ve eder, I Farisæere! thi I give Tiende af Mynte og Rude og alle Haande Urter og forbigaa Retten og Kærligheden til Gud; disse Ting burde man gøre og ikke forsømme hine.
43 Kaitonku Farisawa, domin kuna so a ba ku wuraren zama masu kyau a cikin masujadai, a kuma yi maku gaisuwar bangirma a cikin kasuwanni.
Ve eder, I Farisæere! thi I elske den fornemste Plads i Synagogerne og Hilsenerne paa Torvene.
44 Kaiton ku, gama kuna kama da kabarbarun da ba yi masu shaida ba, mutane kuwa suna tafiya akansu ba tare da saninsu ba.”
Ve eder, thi I ere som de ukendelige Grave, og Menneskene, som gaa over dem, vide det ikke.”
45 Wani malami a cikin shari'ar Yahudawa ya amsa masa ya ce, “Malam, abin da ka ce ya bata mana rai mu ma.”
Men en af de lovkyndige svarede og siger til ham: „Mester! idet du siger dette, forhaaner du ogsaa os.”
46 Sai Yesu ya ce, “Kaitonku malaman shari'a! Gama kun dora wa mutane kaya mai nauyi wanda ya fi karfinsu dauka. Amma ku, ko da dan yatsa ba ku taba kayan ba.
Men han sagde: „Ve ogsaa eder, I lovkyndige! thi I lægge Menneskene Byrder paa, vanskelige at bære, og selv røre I ikke Byrderne med een af eders Fingre.
47 Kaiton ku, gama kuna gina abubuwan tunawa a kabuburan annabawa, alhali kuwa kakanni-kakanninku ne suka kashe su.
Ve eder! thi I bygge Profeternes Grave, og eders Fædre sloge dem ihjel.
48 Ya zama kenan kuna sane da ayyukan kakanni-kakanninku, domin sune suka kashe annabawan da kuke tunawa da su.
Altsaa ere I Vidner og samtykke i eders Fædres Gerninger; thi de sloge dem ihjel, og I bygge.
49 Saboda wannan daliline hikimar Allah ta ce, ''Zan aika manzanni da annabawa a wurinsu, kuma za su tsananta masu har ma za su kashe wadansu daga cikinsu.'
Derfor har ogsaa Guds Visdom sagt: Jeg vil sende Profeter og Apostle til dem, og nogle af dem skulle de slaa ihjel og forfølge,
50 Wannan tsarar, za ta dauki alhakin jinin dukan annabawan da aka kashe tun kafuwar duniya.
for at alle Profeternes Blod, som er udøst fra Verdens Grundlæggelse, skal kræves af denne Slægt,
51 Tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya wanda aka kashe tsakanin bagadi da wuri mai tsarki. I, na gaya ma ku za a nemi hakin su a wurin wannan tsarar
fra Abels Blod indtil Sakarias's Blod, som blev dræbt imellem Alteret og Templet; ja, jeg siger eder: Det skal kræves af denne Slægt.
52 Kaitonku malaman shari'a na Yahudawa, domin kun dauke mabudin sani, ku da kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana masu shiga su shiga.”
Ve eder, I lovkyndige! thi I have taget Kundskabens Nøgle; selv ere I ikke gaaede ind, og dem, som vilde gaa ind, have I forhindret.”
53 Bayan da Yesu ya bar nan wurin, Marubuta da Farisawa suka yi gaba da shi, suka yi jayayya da shi a kan abubuwa da yawa,
Og da han var gaaet ud derfra, begyndte de skriftkloge og Farisæerne at trænge stærkt ind paa ham og at lokke Ord af hans Mund om flere Ting;
54 suna kokari su kafa masa tarko domin su kama shi a cikin kalmomin da yake fadi.
thi de lurede paa ham for at opfange noget af hans Mund, for at de kunde anklage ham.