< Luka 1 >
1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Seeing that many have attempted to draw up a narrative of the facts which are received with full assurance among us
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
on the authority of those who were from the beginning eye-witnesses and were devoted to the service of the divine Message,
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
it has seemed right to me also, after careful investigation of the facts from their commencement, to write for you, most noble Theophilus, a connected account,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
that you may fully know the truth of the things which you have been taught by word of mouth.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
There was in the time of Herod, the king of Judaea, a priest of the name of Zechariah, belonging to the class of Abijah. He had a wife who was a descendant of Aaron, and her name was Elizabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
They were both of them upright before God, blamelessly obeying all the Lord's precepts and ordinances.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
But they had no child, because Elizabeth was barren; and both of them were far advanced in life.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Now while he was doing priestly duty before God in the prescribed course of his class,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
it fell to his lot--according to the custom of the priesthood--to go into the Sanctuary of the Lord and burn the incense;
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
and the whole multitude of the people were outside praying, at the hour of incense.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Then there appeared to him an angel of the Lord standing on the right side of the altar of incense;
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
and Zechariah on seeing him was agitated and terrified.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the angel said to him, "Do not be afraid, Zechariah, for your petition has been heard: and your wife Elizabeth will bear you a son, and you are to call his name John.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Gladness and exultant joy shall be yours, and many will rejoice over his birth.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
For he will be great in the sight of the Lord; no wine or fermented drink shall he ever drink; but he will be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Many of the descendants of Israel will he turn to the Lord their God;
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
and he will be His forerunner in the spirit and power of Elijah, to turn fathers' hearts to the children, and cause the rebellious to walk in the wisdom of the upright, to make a people perfectly ready for the lord."
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
"By what proof," asked Zechariah, "shall I know this? For I am an old man, and my wife is far advanced in years."
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
"I am Gabriel, who stand in the presence of God," answered the angel, "and I have been sent to talk with you and tell you this good news.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
And now you will be dumb and unable to speak until the day when this has taken place; because you did not believe my words--words which will be fulfilled at their appointed time."
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Meanwhile the people were waiting for Zechariah, and were surprised that he stayed so long in the Sanctuary.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
When, however, he came out, he was unable to speak to them; and they knew that he must have seen a vision in the Sanctuary; but he kept making signs to them and continued dumb.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
When his days of service were at an end, he went to his home;
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
and in course of time his wife Elizabeth conceived, and kept herself secluded five months.
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
"Thus has the Lord dealt with me," she said, "now that He has graciously taken away my reproach among men."
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Now in the sixth month the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
to a maiden betrothed to a man of the name of Joseph, a descendant of David. The maiden's name was Mary.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
So Gabriel went into the house and said to her, "Joy be to you, favoured one! the Lord is with you."
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
She was greatly agitated at his words, and wondered what such a greeting meant.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
But the angel said, "Do not be frightened, Mary, for you have found favour with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
You will conceive in your womb and bear a son; and you are to call His name JESUS.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
He will be great and He will be called 'Son of the Most High.' And the Lord God will give Him the throne of His forefather David;
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
and He will be King over the House of Jacob for the Ages, and of His Kingdom there will be no end." (aiōn )
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
"How can this be," Mary replied, "seeing that I have no husband?"
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
The angel answered, "The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you; and for this reason your holy offspring will be called 'the Son of God.'
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
And see, your relative Elizabeth--she also has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
For no promise from God will be impossible of fulfilment."
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
"I am the Lord's maidservant," Mary replied; "may it be with me in accordance with your words!" And then the angel left her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Not long after this, Mary rose up and went in haste into the hill country to a town in Judah.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Here she came to the house of Zechariah and greeted Elizabeth;
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
and as soon as Elizabeth heard Mary's greeting, the babe leapt within her. And Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
and uttered a loud cry of joy. "Blest among women are you," she said, "and the offspring of your body is blest!
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
But why is this honour done me, that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For, the moment your greeting reached my ears, the babe within me leapt for joy.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
And blessed is she who has believed, for the word spoken to her from the Lord shall be fulfilled."
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Then Mary said: "My soul extols the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
And my spirit triumphs in God my Saviour;
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Because He has not turned from His maidservant in her lowly position; For from this time forward all generations will account me happy,
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Because the mighty One has done great things for me--Holy is His name!--
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
And His compassion is, generation after generation, Upon those who fear Him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
He has manifested His supreme strength. He has scattered those who were haughty in the thoughts of their hearts.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
He has cast monarchs down from their thrones, And exalted men of low estate.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
The hungry He has satisfied with choice gifts, But the rich He has sent empty-handed away.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
His servant Israel He has helped, Remembering His compassion--
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
In fulfillment of His promises to our forefathers--For Abraham and his posterity for ever." (aiōn )
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
So Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned home.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Now when Elizabeth's full time was come, she gave birth to a son;
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
and her neighbours and relatives heard how the Lord had had great compassion on her; and they rejoiced with her.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
And on the eighth day they came to circumcise the child, and were going to call him Zechariah, after his father.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
His mother, however, said, "No, he is to be called John."
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
"There is not one of your family," they said, "who has that name."
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
They asked his father by signs what he wished him to be called.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
So he asked for a writing-tablet, and wrote, "His name is John." And they all wondered.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Instantly his mouth and his tongue were set free, and he began to speak and bless God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
And all who lived round about them were filled with awe, and throughout the hill country of Judaea reports of all these things were spread abroad.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
All who heard the story treasured it in their memories. "What then will this child be?" they said. For the lord's hand was indeed with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
And Zechariah his father was filled with the Holy Spirit, and spoke in a rapture of praise.
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
"Blessed be the Lord, the God of Israel," he said, "Because He has not forgotten His people but has effected redemption for them,
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
And has raised up a mighty Deliverer for us In the house of David His servant--
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
As He has spoken from all time by the lips of His holy Prophets-- (aiōn )
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
To deliver us from our foes and from the power of all who hate us.
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
He dealt pitifully with our forefathers, And remembered His holy covenant,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
The oath which He swore to Abraham our forefather,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
To grant us to be rescued from the power of our foes And so render worship to Him free from fear,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
In piety and uprightness before Him all our days.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
And you moreover, O child, shall be called Prophet of the Most High; For you shall go on in front before the Lord to prepare the way for Him,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
To give to His People a knowledge of salvation In the forgiveness of their sins,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Through the tender compassion of our God, Through which the daybreak from on high will come to us,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
Dawning on those who now dwell in the darkness and shadow of death--To direct our feet into the path of peace."
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
And the child grew and became strong in character, and lived in the Desert till the time came for him to appear publicly to Israel.